Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Taminu Turaki ya ce hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi kadan ta zabar wa jam’iyyar PDP shugabanni.
Sakataren yada labarai na kasa na jam’iyya, Ini Ememobong, ya bayyana haka yayin da yake mayar da martani ga taron tuntuba tsakanin INEC da jam’iyyun siyasa, wanda kwamitin rikon kwarya na kasa karkashin jagorancin Abdulraman Mohammed ya halarta.
- Karfafa Tsarin Kimiyyar Fintech A Nijeriya
- Amurka Za Ta Koro ‘Yan Nijeriya 97 Saboda Karya Ka’idojin Shige Da Fice
“Mun san cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta gayyaci shugabannin jam’iyyun siyasa zuwa wani taro.
“Haka kuma muna sane da cewa INEC ta mika gayyata ga wasu tsofaffin ‘yan jam’iyyarmu wadanda ke ikirarin cewa suna shugabanni, don wakiltar jam’iyyarmu, alhali babu irin wannan tanadi a cikin kundin tsarin mulkinmu.
“Wannan mataki, ko da yake a al’ada yana haifar da damuwa kuma zai iya haifar da yaduwar rashin zaman lafiya, za a fuskance shi da dukkan matakan shari’a da ake iya dauka.
“Ko da yake ba abin mamaki ba ne daga wannan shugabancin INEC na yanzu, amma ana sa ran cewa alkali shari’a mara son zuciya zai lura da rashin adalci tare da warware matsalar a kotun daukaka kara.
“Wannan ya hada da hukuncin da suke dogaro da shi, wanda idan an yanke, zai shafi batun da ake dubawa kuma suna yin taka-tsantsan kan lamarin.
“Za mu iya tabbatar da cewa INEC ba ta isa ta zaba mana shugabannin jam’iyyarmu ba,” in ji Ememobong.
Ya yi kira ga dukkan ‘yan PDP su kasance cikin natsuwa da fatan alheri cewa cikin kankanin lokaci, kotun daukaka kara za ta saurari shari’arsu kuma ta yanke hukunci a dukkan shari’o’in da suka shafi shugabancin jam’iyyar.
“Muna tabbatar da cewa ayyukan sake farfadowar jam’iyyarmu, karkashin jagorancin kwararre shugabanmu, Tanimu Turaki, yana tafiya lafiya yadda aka tsara kuma cikin kwanciyar hankali za a warware dukkan matsalolin jam’iyyarmu.
“A karshe zai shawo kan dukkan wadannan kalubalen, don gabatar da jam’iyya mai karfi da hadin kai ga ‘yan Nijeriya, a matsayin sahihin zabin sauya jam’iyya mai mulki,” in ji shi.















Discussion about this post