Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan rikicin cikin gida na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya hana Ministan Abuja, Nyesom Wike, samun cikakken iko da jam’iyyar. Ya ce duk da cewa babu ɓangaren da ya samu cikakkiyar nasara, amma sun samu abin da suke so na hana wani ɓangare mamaye PDP.
Gwamnan ya bayyana cewa halin da PDP ke ciki a yanzu ya sa dole su ɗauki sabon mataki, inda ya ce su da magoya bayansu na shirin ficewa daga jam’iyyar domin samun damar tsayawa takara a zaben 2027. Ya kara da cewa sun riga sun fara tattaunawa da wasu jam’iyyu domin samar wa mabiyansu mafita.
Ya kuma bayyana cewa duk da shirin ficewa daga PDP, zuciyarsu na nan tare da jam’iyyar, amma yanayin siyasa da lokaci ba su ba su damar ci gaba da tsayawa a cikinta ba. A cewarsa, dole ne su ɗauki matakin da zai ba su damar shiga zaɓe cikin sauki.
Dangane da shirinsa na siyasa, Gwamna Bala Mohammed ya tabbatar da cewa zai tsaya takarar Sanatan Bauchi ta Kudu a zaben 2027 a wata jam’iyya daban. Ya ce ya yanke wannan shawara ne bayan kiraye-kirayen da ya samu daga jama’a.
A ƙarshe, ya zargi wasu ɓangarori da ƙoƙarin hana ‘yan adawa damar shiga zaɓe, yana mai cewa dole ne su yi amfani da dabaru da hikima domin tabbatar da cewa magoya bayansu sun samu damar shiga takara da fafatawa a zaɓukan da ke tafe.















Discussion about this post