Idan an sa “ciniki tsakanin Afirka da Sin” a shafin Google don duba bayanai masu nasaba da kalmomin, to, za a ga bayanan da AI na Google ya samar, galibi bisa tushen labaran da kafofin yada labarai na kasashen yammacin duniya suka watsa, sun shafi “karuwar adadin ciniki”, gami da “habakar gibin da kasashen Afirka ke fuskanta yayin da suke ciniki da kasar Sin”. Kamar yin ciniki da kasar Sin zai sa kasashen Afirka gamuwa da hasara. Amma shin batun haka yake?
Jimillar cinikin da aka yi tsakanin Afirka da Sin a shekarar 2025 sun nuna cewa, idan an tantance su bisa darajar kayayyaki, to, za a ga kaso 75% na kayayyakin da kasar Sin ta fitar zuwa kasashen Afirka, su ne injuna, da sassansu, da na’urorin latironi, da sinadaran da ake bukata wajen sarrafa wasu kayayyaki, da dai sauransu. Wadannan kayayyaki ana kiransu “kayayyaki na matakin tsakiya”, domin ba su kai zama kayayyaki na karshe ba tukuna. Sa’an nan a masana’antun kasashen Afirka, an ci gaba da sarrafa wadannan kayayyaki, don mayar da su kayan karshe. Ta wannan hanya, an haifar wa kasashen Afirka karuwar GDP, da ci gaban masana’antu, da karin guraben aikin yi, gami da damar shiga tsarin samar da kayayyaki na duniya.
Wani masanin ilimin tattalin arziki da ke aiki a jami’ar Abuja ta kasar Najeriya, Kennedy Kenchuks Chukwueme, ya taba gaya ma ‘yan jaridan kasar Sin cewa, idan wata kasa ta fi shigar da “kayayyaki na matakin tsakiya” daga kasashen waje, to, ko da yake tana fuskantar gibin ciniki, hakan zai tabbatar da makomarta ta inganta bangaren masana’antu. Ya ce, misali, kayayyakin aikin gini, da injuna da ake shigar da su daga kasar Sin zuwa Najeriya, sun samar da damar tsimin kudi yayin da ake gina tashohin jiragen ruwa, da layin dogo a Najeriya, gami da taimakawa Najeriya raya masana’antu, da inganta aikin fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin ketare.
Yayin da ake tantance cinikin da ake yi tsakanin Afirka da Sin, bai kamata a lura da gibin ciniki da ake samu ba kawai, maimakon haka, ya kamata a kara mai da hankali kan yanayin taimakawa juna na tsare-tsaren tattalin arzikin Afirka da Sin.
Afirka har yanzu tana wani mataki na farko a fannin raya masana’antu, saboda haka, nahiyar ta fi fitar da makamashi, da ma’adinai, da amfanin gona zuwa ketare. A nata bangare, kasar Sin ta kware a fannin masana’antu na zamani, don haka tana iya samar da dimbin “kayayyaki na matakin tsakiya” ga kasashen Afirka, a kokarin biyan bukatarsu ta raya masana’antu. Bisa hadin gwiwar Afirka da Sin, idan kasashen Afirka za su iya zamanantar da tsarin hada-hadar samar da kaya, da kyautata muhallin zuba jari a-kai-a-kai, to, tabbas za su samu sakamako mai gamsarwa, wanda zai kunshi ci gaban tattalin arzikin dukkan bangarorin Afirka da Sin, da damar tabbatar da moriyar junansu. (Bello Wang)














