ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Ciniki A Tsakanin Afirka Da Sin Za Ta Tabbatar Da Moriyar Junansu

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 month ago
default

default

Idan an sa “ciniki tsakanin Afirka da Sin” a shafin Google don duba bayanai masu nasaba da kalmomin, to, za a ga bayanan da AI na Google ya samar, galibi bisa tushen labaran da kafofin yada labarai na kasashen yammacin duniya suka watsa, sun shafi “karuwar adadin ciniki”, gami da “habakar gibin da kasashen Afirka ke fuskanta yayin da suke ciniki da kasar Sin”. Kamar yin ciniki da kasar Sin zai sa kasashen Afirka gamuwa da hasara. Amma shin batun haka yake? 

Jimillar cinikin da aka yi tsakanin Afirka da Sin a shekarar 2025 sun nuna cewa, idan an tantance su bisa darajar kayayyaki, to, za a ga kaso 75% na kayayyakin da kasar Sin ta fitar zuwa kasashen Afirka, su ne injuna, da sassansu, da na’urorin latironi, da sinadaran da ake bukata wajen sarrafa wasu kayayyaki, da dai sauransu. Wadannan kayayyaki ana kiransu “kayayyaki na matakin tsakiya”, domin ba su kai zama kayayyaki na karshe ba tukuna. Sa’an nan a masana’antun kasashen Afirka, an ci gaba da sarrafa wadannan kayayyaki, don mayar da su kayan karshe. Ta wannan hanya, an haifar wa kasashen Afirka karuwar GDP, da ci gaban masana’antu, da karin guraben aikin yi, gami da damar shiga tsarin samar da kayayyaki na duniya. 

Wani masanin ilimin tattalin arziki da ke aiki a jami’ar Abuja ta kasar Najeriya, Kennedy Kenchuks Chukwueme, ya taba gaya ma ‘yan jaridan kasar Sin cewa, idan wata kasa ta fi shigar da “kayayyaki na matakin tsakiya” daga kasashen waje, to, ko da yake tana fuskantar gibin ciniki, hakan zai tabbatar da makomarta ta inganta bangaren masana’antu. Ya ce, misali, kayayyakin aikin gini, da injuna da ake shigar da su daga kasar Sin zuwa Najeriya, sun samar da damar tsimin kudi yayin da ake gina tashohin jiragen ruwa, da layin dogo a Najeriya, gami da taimakawa Najeriya raya masana’antu, da inganta aikin fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin ketare. 

ADVERTISEMENT

Yayin da ake tantance cinikin da ake yi tsakanin Afirka da Sin, bai kamata a lura da gibin ciniki da ake samu ba kawai, maimakon haka, ya kamata a kara mai da hankali kan yanayin taimakawa juna na tsare-tsaren tattalin arzikin Afirka da Sin. 

Afirka har yanzu tana wani mataki na farko a fannin raya masana’antu, saboda haka, nahiyar ta fi fitar da makamashi, da ma’adinai, da amfanin gona zuwa ketare. A nata bangare, kasar Sin ta kware a fannin masana’antu na zamani, don haka tana iya samar da dimbin “kayayyaki na matakin tsakiya” ga kasashen Afirka, a kokarin biyan bukatarsu ta raya masana’antu. Bisa hadin gwiwar Afirka da Sin, idan kasashen Afirka za su iya zamanantar da tsarin hada-hadar samar da kaya, da kyautata muhallin zuba jari a-kai-a-kai, to, tabbas za su samu sakamako mai gamsarwa, wanda zai kunshi ci gaban tattalin arzikin dukkan bangarorin Afirka da Sin, da damar tabbatar da moriyar junansu. (Bello Wang) 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
  • Sulaiman
    “Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa
  • Sulaiman
    Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sarkin Musulmi Ya Buƙaci A Binciki Yadda Aka Harbe Kanar AbdulKarim Ode A Abuja

Sarkin Musulmi Ya Buƙaci A Binciki Yadda Aka Harbe Kanar AbdulKarim Ode A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.