• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Dausayin Musulunci

Hunkuncin Sauke Wa Mamaci Alkur’ani Bayan Ya Mutu

by Dakta Jamil Zarewa
4 months ago
in Dausayin Musulunci
0
Hunkuncin Sauke Wa Mamaci Alkur’ani Bayan Ya Mutu

Assalamu alaikum. Wai Malam Meye Hukuncin Sauke wa Mamaci Al-kur’ani?

Wa’alaikum assalam. To malamai sun yi sabani akan wannan mas’ala zuwa maganganu guda uku:

  • Me Ya Sa Erik Ten Hag Yake Goyon Bayan Harry Maguire? 
  • Wakilin Sin Ya Yi Cikakken Bayani Kan Sakamakon Da Jihar Xinjiang Ta Samu Wajen Kare Hakkin Bil Adam

1. Bai halatta ba, saboda ba’a samu wani nassi da yake nuni zuwa haka ba, kuma ita ibada ba’a yinta sai da nassi na musamman, sannan kuma mutum ba shi da wani abu sai aikinsa, kamar yadda aya ta 39 da take cikin suratu Najm, take nuni zuwa haka, tun da ba’a samu ba, yin hakan zai zama bidi’a, wannan ita ce maganar farko ta Shafi’i.

2. Ya halatta ayi, saboda hadisan da suke nuna cewa mamacin yana iya amfana da abin da mai rai zai masa, kamar hadisan da suka yi umarni da yi masa sallah da nema masa gafara bayan ya mutu, da yi masa sadaka, wannan shi ne maganar mafi yawan malamai, har wasu marubuta ma sun hakaito ijma’i akan haka, saboda mutane sun jima suna yi kuma malamai ba su yi musu inkari ba.

3. Akwai wadanda suka tafi akan cewa: idan dansa na cikinsa ya yi masa, to ladan zai same shi, amma wanda ba dansa ba, ba zai yi masa ba, saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi “Dan mutum yana daga cikin aikinsa” Abudawud ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi a sahihu sunani-abi-dawud hadisi mai lamba ta: 2528.

Labarai Masu Nasaba

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

Hakuri Da Baiwar (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

Saidai wasu malaman, suna rinjayar da magana ta uku, saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: “Idan dan’adam ya rasu ayyukansa sukan yanke sai dayan abubuwa guda uku: sadaka mai gudana, ko ilimin da ake amfana da shi, ko da nagari da yake masa addu’a” kamar yadda Tirmizi ya rawaito shi kuma ya inganta shi a hadisi mai lamba ta: 1376.

Wadancan hadisan kuwa da masu Magana ta biyu suka kafa hujja da su, to za’a yi amfani da su ne a iya inda suka zo, amma ba za’a yi kiyasin karatun kur’ani akan su ba.

Don neman Karin bayani: duba majmu’ul fataawa: 24\366 da Nailul Audaar 4\112 da Ahakamul jana’iz shafi na: 171.

Allah shine mafi sani.

 

Tags: AddiniFatawaManzon Allah SAWMutuwaSauke Alkur'ani
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Na’urar Kuafu-1 Ta Farko Kan Binciken Hasken Rana

Next Post

NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

Related

Dabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa
Dausayin Musulunci

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

2 days ago
Dabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa
Dausayin Musulunci

Hakuri Da Baiwar (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

3 weeks ago
Dabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa
Dausayin Musulunci

Kyawawan Dabi’u Da Hasken Sanin Allah, Halittar Annabawa Ce Ba Koya Suke Ba

2 months ago
Ka’idojin Mu’amala Da Mutane Guda (2)
Dausayin Musulunci

Ka’idojin Mu’amala Da Mutane Guda (2)

2 months ago
Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 
Dausayin Musulunci

Buhari Ya Yi Allah Wadai Da Sace Jarirai Sabbin Haihuwa A Anambra 

2 months ago
Dabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa
Dausayin Musulunci

Kyawawan Halaye 2: Wasu Annabawa Da Sauran Bayin Allah Da Suka Yi Magana A Tsummar Jego

2 months ago
Next Post
NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

LABARAI MASU NASABA

Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

February 6, 2023
Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

Ya Uwargida Za Ta Yi Da Mijin Da Bai Iya Zaman Hira Ba?

February 6, 2023
Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

February 6, 2023
Gwamnonin Kaduna, Kogi Da Zamfara Sun Maka Gwamnati A Kotu Kan Karancin Kudi

Gwamnonin Kaduna, Kogi Da Zamfara Sun Maka Gwamnati A Kotu Kan Karancin Kudi

February 6, 2023
Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa

February 6, 2023
PDP Ta Zargi Tinubu Da APC Kan Boye Sabbin Kudi Don Sayen Kuri’u

PDP Ta Zargi Tinubu Da APC Kan Boye Sabbin Kudi Don Sayen Kuri’u

February 6, 2023
Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

February 6, 2023
2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

February 6, 2023
2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

February 6, 2023
Tashoshin Talabijin 6 Zasu Haska Shiri Na Musanman Kan Rayuwar Shugaba Buhari

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

February 6, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.