ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Indiya Ta Cafke Wasu ‘Yan Nijeriya Uku Da Laifin Zamba Ta Intanet

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Indiya

An kama wasu ‘yan Nijeriya uku a Birnin Delhi kuma za a daure su akalla shekaru uku a gidan yari bisa zargin damfarar wata ‘yar kasar Indiya sama da Naira miliyan 2.62.

Wani rahoto da jaridar The Times of India ta fitar ya bayyana cewa, ‘yansanda masu yaki da aikata laifuka ta Intanet sun cafke Lezhu John, Gibril Mohammed, da Egboola Ekena kan wata shari’a da ta shafi damfarar wata ‘yar Indiya.

  • An Gurfanar Da Wani Mashawarcin Bogi Bisa Zargin Zambar Naira 600,000
  • CIA Na Shirin Kafa Wata Kasa A Cikin Indiya Ne?

Duk da cewa har yanzu ba a gurfanar da mutanen uku a gaban kotu a hukumance ba, binciken da jaridar PUNCH Metro ta gudanar ya nuna cewa idan har aka same su da laifi, kowanne wanda ake tuhuma zai fuskanci hukuncin daurin shekaru akalla uku a gidan yari a karkashin dokar fasahar sadarwa ta IT (IT Act, 2000) da kuma dokar hukunta masu laifi ta Indiya.

ADVERTISEMENT

A cewar sashe na 66D na Dokar IT ta Indiya, kamar yadda aka ambata a shafin Intanet kamfanin lauyoyi na Indiya, S.S. Rana & Co. ranar Lahadi, “Hukuncin yaudarar mutum ta hanyar amfani da kayan aikin kwamfuta; za a hukunta shi da hukuncin dauri na kowane kwatance na tsawon wa’adin, wanda zai iya tsawaita har zuwa shekaru uku, sannan kuma za a ci shi tarar da za ta iya kai har zuwa rupee dubu daya. .”

An zargi wadanda ake zargin da aikata laifin ta’addanci ta yanar gizo wanda ya kai ga mutane da dama a fadin Indiya suka zama wadanda aka kashe.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

A cewar jami’an ‘yansanda masu yaki da aikata laifuka ta Intanet a Indiya, sun ce wacce aka damfara din a baya-bayan nan ta shigar da kara a ofishin ‘yansanda ta intanet bayan ta fahimci cewa an damfare ta hanyar amfani da shafinta na Instagram.

Rahotanni sun bayyana cewa wadanda ake zargin suna da hotuna da dama na maza da mata da aka ajiye a cikin wayoyinsu na hannu, wadanda ake zargin sun yi amfani da su wajen kirkirar shafukan sada zumunta na bogi da yaudarar mutane.

“Bincike ya nuna cewa wadanda ake tuhumar suna amfani da asusun banki sama da 500 wajen aikata zamba. Sama da korafe-korafe 900 ne aka shigar a fadin kasar nan dangane da wadannan asusun ajiyar banki,” in ji ACP (Cybercrime), Badodara, M.M. Rajput.

Daya daga cikin wadanda ake tuhumar ya bayyana kansa a matsayin Sohn Yunmin, inda ya ce shi injiniyan sinadarai ne daga Amurka.

Wanda ake zargin ya shaida wa matar nan ba da jimawa ba zai yi aiki a Assam, kuma ta hanyar abokantakar da suke da shi, ta aika masa da kyauta.

Rahoton ya kara da cewa, “A cikin watan Afrilun wannan shekara, wanda ake zargin ya shaida wa matar cewa yana bukatar ya sayi wasu injina kuma abokinsa wanda ya kamata ya biya kudinsa, ba shi da kudi a asusun ajiyarsa na banki. Ya nemi ta canza masa 50,000. Bayan wasu kwanaki, wanda ake tuhumar ya gaya mata yana zuwa Assam saboda ya sami tayin aiki a can kuma kunshin nasa zai sauka a Indiya.

“Bayan wasu kwanaki, sai ta samu waya daga wata mata mai suna Niharika, inda ta nemi kudi Naira 35,500 kan jakar da ke da Dalar Amurka. Ta tura kudin, amma Niharika ta ci gaba da neman karin kudi ta hanyar ba da dalilai daban-daban. Mai shigar da karar ya kare ya mika mata Naira 1.69, amma nan da nan ta gane cewa ana yaudararta.

Rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa, an gano wadanda ake zargin ne ta hanyar amfani da bayanan mu’amalar bankin. Har yanzu dai ba a san lokacin da za a gurfanar da ‘yan Nijeriya uku a gaban kotu ba.

Indiya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Indiya
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Indiya
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Indiya
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Kakaki: Tafarnuwa Ba Ta Taba Tunanin Za Ta Iya Yin Babbar Barazana Ga Amurka Ba

Kakaki: Tafarnuwa Ba Ta Taba Tunanin Za Ta Iya Yin Babbar Barazana Ga Amurka Ba

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.