ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Neman Zunzurutun Kudi Kimanin Naira Tiriliyan 1 Don Gudanar Da Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
4 months ago
inec

Hukumar zaBe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanar da majalisar kasa cewa tana bukatar naira biliyan 873.78 don gudanar da zaBen 2027. Haka nan kuma hukumar ta bukaci karin naira biliyan 171 don taimaka wa ayyukanta a shekarar 2026.

Naira biliyan 873.78 da aka tsara don gudanar da zaBukan shekarar 2027 yana nuni da karuwa mai yawa daga naira biliyan 313.4 da gwamnatin tarayya ta saki don gudanar da zaBen g 2023.

  • Tsarin Siyasar Kano: Ya Kamata Gwamna Abba Ya Yunkura…
  • Sashen Sayayya Da Kashe Kudade Na Kasar Sin Na Samun Bunkasa Ba Tare Da Tangarda Ba A Hutun Bikin Bazara

Kasar za ta gudanar da zaBe a shekarar 2027, yayin da jihohin Ekiti da Osun za su gudanar da zaBen gwamna a wannan shekarar, tare da zaBen shugabannin kananan hukumomi a Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma zaBen cike gurbi.

ADVERTISEMENT

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya bayyana wannan yayin da yake gabatar da kasafin kudin hukumar na 2026 da kuma kiyasin kashe kudi don zaBukan 2027 a gaban kwamitin hadin gwiwa na majalisar dokoki kan harkokin zaBe a Abuja.

A cewar Amupitan, kasafin kudin zaBe na naira biliyan 873.78 ya kunshi gudanar da dukkan zaBukan 2027, yayin da naira biliyan 171 ta 2026 za ta tallafa wa ayyukan yau da kullum, ciki har da zaBukan cike gurbi da zaBukan gwamnoni a wannan shekarar.

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

A cewarsa, kasafin kudin zaBe da aka gabatar bai hada da sabon bukata daga hukumar kula da masu yi wa kasa hidima (NYSC) ba, wanda ta neman karin alawus ga masu yi wa kasa hidima da ke aiki a matsayin ma’aikata na wucin gadi a lokacin zaBe.

Ya bayyana cewa duk da cewa ba a gabatar da cikakkun bayanai na wasu batutuwan ba, kasafin kudin zaBen na kusan naira tiriliyan 1 an tsara shi a cikin manyan sassa biyar.

“Naira biliyan 379.75 an ware su ne don gudanar da ayyukan yau da kullum, naira biliyan 92.32 an ware su ne don ayyukan gudanarwa, naira biliyan 209.21 an ware su ne don kudaden da za a kashe a Bangaren fasaha, naira biliyan 154.91 don kudaden da za a kashe na babban zaBe da kuma naira biliyan 42.61 don kudade zarga-zirgan ma’aikata,” in ji Amupitan.

Ya bayyana cewa an shirya kasafin kudi a bisa tsarin sashe na 3(3) na dokar zaBe ta 2022, wanda ya umurci hukumar da ta shirya kasafin kudin zaBe akalla shekara guda kafin babban zaBe.

A 2026, Amupitan ya bayyana cewa ma’aikatar kudi ta bayar da kasafin kudi na naira biliyan 140, amma ya kara da cewa INEC na ba da shawarar jimillar kashe kudi na naira biliyan 171.

Jimillar kudaden ya hada da naira biliyan 109 kudin ma’aikata da naira biliyan 18.7 don ayyukan yau da kullum, da naira biliyan 42.63 don ayyukan da suka shafi zaBe da naira biliyan 1.4 don gudanar da manyan ayyuka.

Har ila yau, ya gano rashin samun cibiyar sadarwa ta musamman a matsayin babban kalubale na aikin hukumar. Yana kara da cewa idan hukuamar ta haBaka nata tsarin hanyar sadarwa, ‘yan Nijeriya za su kasance cikin yanayi mai kyau wajen sa idan akwai wata matsala ta fasahar sadarwa.

A yayin jawabi a zaman, Sanata Adams Oshiomhole ya ce ka da hukumomin waje su tsara tsarin kasafin kudi ga INEC, la’akari da muhimmancin aikin da take da shi. Ya yi kira a ajiye tsarin kasafin kudi mai rikitarwa.

Ya yi kira ga majalisar kasa ta hada kai da Shirin kudi na INEC don kauce wa yiwuwar karancin kudi a lokacin gudanar da zaBe.

Haka kuma, wani dan majalisar wakilai daga Jihar Edo, Billy Osawaru, ya nemi a sanya kasafin kudin INEC a kan babban jigo kamar yadda kundin tsarin mulkin ya tanada, tare da sakin kudin gaba daya a kan lokaci domin ba da damar yin shiri zaBen 2027 a kan lokacin da ya dace.

Kwamitin hadin gwiwa ya amince da wani kudiri da ke ba da shawarar sakin kasafin kudin shekara-shekara na kwamitin sau daya.

Kwamitin ya kuma ce zai duba bukatar NYSC na kimanin naira biliyan 32 don kara kudin alawus din mambobin hukumar zuwa naira 125,000 kowanne lokacin da aka dauke su don ayyukan zaBe.

Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan INEC, Simon Lalong, ya tabbatar da cewa majalisa za ta yi aiki tare da hukumar don tabbatar da cewa ta samu goyon bayan da ya dace wajen gudanar da zaBen 2027 cikin nasara.

Haka kuma, shugaban kwamitin majalisar dokoki kan al’amuran zaBe, Bayo Balogun, ya yi alkawarin goyon bayan dokokin amma ya yi gargadi ga kwamitin ka da ya dauki alkawuran da zai iya kasa cikawa.

Ya tuna cewa a lokacin zaBen 2023, INEC ta bayar da tabbacin cewa za a dora sakamakon zaBe a shafi INEC, wanda hakan ya tabbacin da cewa ana iya sa ido kan sakamakon zaBe a kan lokaci.

“Na’urar saka sakamakon zaBe ba ya cikin dokar zaBe ko kadan, yana cikin dokokin INEC ne kawai. Don haka, a yi hattara yadda za a yi alkawaruka,” in ji Balogun.

Inec
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Inec
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin
Manyan Labarai

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026
Next Post
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamnan Radda Ya Rantsar Da Sabon Mai Shari’a, Khadi Mustapha Salisu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.