Kasar Iran ta bayyana cewa ba ta da shirin halartar zagaye na gaba na tattaunawa da Amurka da za a yi a Pakistan, yayin da rikici ke ƙara tsananta tsakanin ɓangarorin biyu. Kafafen yaɗa labaran gwamnatin ƙasar sun ruwaito cewa babu wani shiri a halin yanzu na shiga tattaunawar, duk da yunƙurin Shugaban Amurka, Donald Trump, na tura tawaga zuwa Pakistan.
Matakin ya biyo bayan taƙaddama kan takunkumin ruwa da Amurka ke ƙaƙabawa tashoshin jiragen ruwan Iran, wanda ya ƙara tsananta bayan wani jirgin ruwan yaƙin Amurka ya harba tare da kama wani jirgin Iran da ake zargin ya karya takunkumin. Iran ta yi alƙawarin ɗaukar matakin ramuwar gayya, inda aka ruwaito cewa ta tura jirage marasa matuƙi zuwa ga jiragen yaƙin Amurka.
- Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
- Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
- Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri
- Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
- ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa
Rahotanni daga majiyoyin Iran sun nuna cewa yanayin tattaunawar ba shi da kyau, inda suka jaddada cewa dole ne a janye takunkumin Amurka kafin a samu ci gaba mai ma’ana. Haka kuma, kafafen yaɗa labaran gwamnati sun soki buƙatun Amurka, suna mai cewa ba su da ma’ana, tare da cewa babu tabbacin samun nasarar tattaunawa a irin wannan yanayi.
Duk da cewa an taɓa bude mashigar Hormuz na ɗan lokaci bayan tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hezbollah, Iran ta sake rufe ta sakamakon ci gaba da takunkumin Amurka. A yayin da Amurka ke ci gaba da matsin lamba, Iran ta musanta zargin cewa za ta miƙa wasu sinadarai na uranium, tana mai cewa hakan bai taba kasancewa cikin tattaunawa ba, yayin da ake ƙara tsaurara matakan tsaro a Pakistan gabanin shirin ganawar.














