Kafafen yada labaran gwamnatin Iran sun bayyana cewa an sake sanya mashigar ruwa ta Strait of Hormuz karkashin tsauraran matakai, lamarin da ke takaita zirga-zirga, bayan da kasar ta zargi Amurka da kasa cika alkawarin janye takunkumin ruwa da aka kakaba wa tashoshinta. Gidan talabijin na gwamnati, IRIB, ya ce yanzu mashigar ta sake zama karkashin kulawa mai tsauri, inda duk wata zirga-zirga ke bukatar amincewar Iran.
Matakin ya biyo bayan dan takaitaccen bude mashigar da aka yi sakamakon tsagaita wuta na kwanaki 10 tsakanin Isra’ila da Lebanon, wanda ya haifar da fatan daidaita harkokin samar da man fetur a duniya. Sai dai rundunar hadin gwiwar sojin Iran ta bayyana cewa mashigar ta koma yadda take a baya saboda Amurka ta ki janye takunkumin da take kakabawa harkokin ruwa na kasar.
- Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
- Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote
- Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
- Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato
- Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
A cikin wata sanarwa, sojojin Iran sun ce sun amince da barin wasu jiragen dakon mai da na kasuwanci su rika wucewa bisa yarjejeniya, amma Amurka ta ci gaba da abin da suka kira takunkumi. Sun jaddada cewa muddin ba a ba da cikakkiyar ‘yancin zirga-zirga ga jiragen ruwa daga Iran da zuwa Iran ba, mashigar za ta ci gaba da kasancewa karkashin cikakken iko da kulawar sojojin kasar.
Mashigar Hormuz na daya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar man fetur a duniya, kuma an riga an ayyana ta a matsayin rufaffiya tun bayan hare-haren sojin Amurka a ranar 28 ga Fabrairu. Duk da dan farfadowar zirga-zirga da aka gani kwanan nan, ana sa ran sabbin matakan za su sake girgiza kasuwannin makamashi, yayin da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya jaddada cewa takunkumin da aka kakaba zai ci gaba har sai an cimma cikakkiyar yarjejeniya.














