Tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Seriake Dickson, ya bayyana jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) a matsayin jam’iyya mai cikakken kwanciyar hankali wadda ba ta da rikice-rikicen shari’a ko bangaranci.
Dickson ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, da kuma takwaransa na Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, zuwa jam’iyyar. Ya ce duk da cewa NDC sabuwar jam’iyya ce, amma tana da ƙarfin da zai ba ta damar taka rawa a siyasar ƙasa.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar ita ce mafi saurin bunƙasa a Nijeriya, kuma ba ta san abin da ake kira rikicin cikin gida ko shari’a a kotu ba. A cewarsa, mambobin jam’iyyar sun nuna ƙwarin gwuiwa da amincewa da manufarta duk da ƙalubalen da ke akwai.
A nasa ɓangaren, Peter Obi ya buƙaci gwamnatin tarayya da kada ta shigar da rikicin siyasa cikin NDC, yana mai kira ga shugabannin siyasa da su mutunta tsarin dimokuraɗiyya tare da gujewa haddasa rikici a jam’iyyun adawa.
Shi ma Rabiu Musa Kwankwaso ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi rajista da NDC cikin gaggawa, yana mai bayyana cewa tuni ɓangarensa na siyasa ya fara shiga jam’iyyar domin ƙarfafa tsarinta da faɗaɗa ƙarfinta a faɗin ƙasa.















Discussion about this post