ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi Sun Samu Kudade Daga Gwamnatin Tinubu Fiye Da Duk Wani Lokaci A Tarihi – Abdulaziz Abdulaziz (2)

by Bello Hamza and Sulaiman
8 months ago
Jihohi

… a ci gaba da hirar da Editanmu Bello Hamza ya yi da mai ba shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu shawara a bangare harkar jarida Abdulazizs Abdulazizs ya bayyana cewa gwamnonin kasar sun samu7 kudaden shiga daha gwamantin tarayya fiye da yadda aka samu samu a shekaru8n baya, wanda haka y6a basu damar gudanar da ayyukan raya nkasa masu dinbin yawa. Haka kuma duk da dimbim matsalolin rashin tsaro da gwamnatinsa ta gada daga gwamnatocin baya, Shugaba Tinubu ya yi rawar gani wajen shawo kan lamarin. Haka kuma ya yi bayanin yadda gwamantin Tinjubu ta farfado da ayyukan da gwamnatocin baya suka yi watsi da su musamman abin da ya shafi manyan hanyoyi a arewacin kasar nan. Ga dai yadda hirar ta kasance.

Don a kan ce wasu jihohin ma abin da suka karba a cikin shekaru biyun nan da doriya, ya nunka kusan abin da wasu jihohin suka karba cikin shekaru takwas.

Kwarai kuwa. Sosai! A jihohi da dama haka abin yake, shiyasa nake fada ai cewa ko hisabi ma za a yi, maganar gaskiya idan za a kyautata aikin da wani gwamna ya yi ko wata gwamnati ta yi a shekara hudu ko a shekara takwas, a ce za a hada da wannan shekara biyun; ai abin ba daya ba ne. Saboda kudaden da aka samu ba kadan ba ne.

ADVERTISEMENT

 

Amma ba a ganin darajar kudin, misali; ayyukan da kudaden za su yi maka a wadancan shekarun, a yanzu watakila sai an kwatanta da na yanzu; duk da yawan kudin?

LABARAI MASU NASABA

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

Ai ‘inflation’ din ya ragu. Akwai lokacin da aka samu matsalar cewa ai kudin ga yawan su, amma darajar ta ragu sosai. Amma yanzu ai darajar kudin ta sake dawowa daidai misali. Ba zance daidai yake ba, gaskiya. Da gaske ne ba daidai yake ba, tun da a wancan lokacin dala tana dari shida da wani abu, amma yanzu tana dubu daya da wani abu, amma ai yawancin abubuwan da muke yi ba na dala ba ne. Yanzu misali ma’aikata da ake dauka ai albashin an kara, amma ba nunkawa aka yi ba. Kuma albashin ma’aikatan idan a da kudin da gwamnati take biya na albashi a wata biliyan biyar ne misali a Kano, to ai yanzu ba wani bambanci ya yi sosai ba, kuma ana biya din, kuma har ana kara daukar ma’aikata.

Duk wannan wani abu ne da yake nuna cewa wato ‘financial engineering’ ne da ake fada a turance; wato sauya fasalin tattalin arzikin Nijeriya da gwamantin Bola Tinbu take yi, yana haifar da da mai ido kwarai da gaske.

Idan ka duba bangaren masu shigo da kudade daga kasashen waje domin su saka jari, ta nan ne ma babban hanyar ma da za ka dubi ci gaban tattalin arzikin. Saboda idan tattalin arzikin ka ba ya yin kyau, ba wanda zai zo. Saboda dan kasuwa ba mai sadaka ba ne, ko mai yin abu saboda Allah. Ba fisabilillah ba. Kasuwanci ne ana yi don riba. Duk wanda zai zo ya saka kudi, yana duba ta ya ya ne zai samu tasiri ya samu alheri daga wannan kudin da ya zuba. To yanzu muna ta samun karuwar sanya hannun jari da ake saukowa; kudade ana ta shigo da su za a kafa kamfani a nan, a’a za a zo a yi abin wutar lantarki, za a zo a yi railway da sauran su. Saboda sun ga cewa tattalin arzikin Nijeriya yana kyau ne.

Yanzu harkar hako mai, da sai da ya zama kamfanukan hakar mai suna ta barin Nijeriya, yanzu kuma suna ta kokarin dawowa ne. Akwai kamfanoni akalla guda biyu zuwa uku, manyan kamfanoni ne wanda a da sun fita ne, yanzu suna rokon za su dawo su ci gaba. Wasun su ma sun dawo.

Daga bayananka duk da ka fadada abubuwa ne da za a iya cewa kusan kafatanin ‘yan Nijeriya na iya ribatar su. Ka yi bayanin wasu kebantattun ayyuka da al’ummar yankin arewa suka amfana; hanyoyi da layin iskar gas da ake janyowa. Amma tattare da hakan, mutanen yankin na ganin an fi karkata ribar da kasar ke ciki ga bangaren Kudanci, watakila saboda shi shugaban kasar daga can ya fito, ko kuma wani abu mai kama da haka.

Wato lokacin da gwamnatin nan ta zo kusan ayyukan more rayuwa da yawa ana gudanar da su a arewacin Nijeriya. Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta bayar da ayyuka. Wadanda wasun su ba a ma fara ba, ko kuma ana kokarin fara su, ko kuma ba a dade da farawa. A Kudu yawanci babu irin wadannan ayyukan. Idan banda idan ka dauki hanyar Legas – Ibadan da kuma wancan gadar da take hada kasar Inyamurai – gabashi da kudancin Nijeriya, wato ‘East-West Road second Niger Bridge’, idan banda wannan wanda yawancin su an gama su ko ana tunanin kammala wa. Amma a nan arewa, nan aka zo aka tarar da ayyuka da yawa, wanda ayyuka ne na kudade masu yawan gaske. Kamar yadda na ce an bayar da su, amma aikin ba su je ko’ina ba. Amma gwamnatin nan ta ci gaba da su.

Abin da mutane suke so shi ne kullum a ce an bayar da aiki a nan kaza, an bayar da aiki a nan kaza. Amma babban abu mafi muhimmanci ga shugaba mai adalci, mai tunani shi ne ya karasa aikin alherin da ya tarar an fara. Ba wai aikin da zai ba shi suna ba, a ce ai shi ya fara wannan aikin.

Mu ba mu damu a ce ai Buhari ne ya fara aikin Kano zuwa Kaduna ba da Abuja ba, ba damuwa. Mu wannan gwamnatin tana son ta ga ta kammala. Idan da wannan gwamnatin tana da niyyar, tana da manakisa tana da niyyar keta, ga arewacin Nijeriya, wadannan ayyuka da dama da muka tarar sai mu bar su, sai a ki kammala su, sai a yi rikon sakainar kashi, sai a yi wassarere, a bar su.

Ka tuna akwai ayyukan da sun fi shekara ashirin ana yin su, misali; titin Abuja zuwa Lokoja, ko titin Kano zuwa Maiduguri. An yi shekaru, wasu tun Obasanjo, wasu tun ‘Yar’adua.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa inshaAllah

Jihohi
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Jihohi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
Tattaunawa

Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

August 28, 2026
Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Tattaunawa

Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

August 20, 2026
Nijeriya
Tattaunawa

2027: Shugaba Mai Gaskiya Da Hangen Nesa Nijeriya Ke Buƙata —Ahmad Shu’aibu

August 8, 2026
Next Post
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

'Yansanda Sun Kama Matashi Mai Shekara 27 Kan Cin Zarafin Yarinyar Makwabta

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.