Gwamnatin tarayya, ta kammala tare kuma da miƙa sabbin cibiyoyi biyu na kula da lafiyar dabbobi na matakin farko.
Ta miƙa su ne ga Jihohin Legas da Ogun, wanda hakan na daga cikin ƙoƙarin da gwamnatin ke ci gaba da yi na ƙara haɓaka fannin na kiwo a faɗin wannan ƙasa.
Cibiyar ta Jihar Legas, ta kasance a yankin Epe, inda kuma ta Ogun ta ke a yankin Ijebu Igbo.
Kazalika, hakan na daga cikin shirin Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon Dabbobi ta Tarayya, na kafa cibiyoyin kula da lafiyar dabbobi a ƙananan hukumomi 774 da ake da su a ƙasar.
A jawabinsa a Epe, a wajen taron miƙa cibiyoyin, Babban Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha ya ce; an samar da tsarin ne, domin cibiyoyin su kasance kusa da masu kiwo da ƙara sanya ido da kuma daƙile yaɗuwar cututtuka a tsakanin dabbobi.
Ministan, wanda daraktan kula da lafiyar dabbobi, Dakta Alao Mitchel ya wakilta, ya ƙara da cewa; ana sa ran shirin, zai ƙara taimakawa, wajen ƙara haɓaka fannin kiwo a ƙasar.
Ita kuwa, daraktar samar da bayanai da huɗɗa da jama’a a Ma’aikatar Henrietta Okokon cewa ta yi, ana kan wanzar da shirin a wasu johohi 20 na wannan ƙasa.
Ta ƙara da cewa, bakwai daga ciki, an gina asibitocin kula da lafiyar dabbobi a Jihohin Sakkwato, Neja, Enugu, Ondo, Borno, Adamawa da kuma Edo, inda ta ƙara da cewa; a yanzu haka, ana shirin ƙara kafa wasu 14.















Discussion about this post