ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 30 Kacal Ne Ke Yin Noma Da Kayan Noma Na Zamani A Nijeriya —AFAN

by Abubakar Abba
2 weeks ago

Ƙungiyar manoma ta ƙasa, reshen Jihar Legas (AFAN), ta yi iƙirarin cewa; kashi talatin cikin ɗari ne kacal na manoman ƙasar ke amfani da kayan aikin noma na zamani.

Ta danganta hakan ne, kan rashin ci gaba da noma amfani gona masu yawa a ɗaukacin faɗin ƙasar.

A cewar ƙungiyar, kimanin kashi 70 na manoman ƙasar, har yanzu suna yin noma ne da kayan gargajiya, wanda a yanzu, kashi 30 kacal ne ke yin amfani da kayan aikin noma na zamani.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban ƙungiyar, Mista Shakin Agbayewa, ya sanar da haka ne a Legas, wanda kuma ya danganta matsalar, kan rashin samun ingattacciyar ƙasar nomar da kuɗaɗe da sauran kayan aikin noma na zamani.

Agbayewa ya koka, kan yadda manoman ƙasar, ba a samar musu da kayan aiki na zamani, kamar taraktocin noma da sauran kayan aikin, na zamani.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A cewarsa, tsadar kuɗin ɗaukar hayar taraktocin noma, wanda hakan ke ci gaba da haifar wa manoman ƙasar, musamman ƙanana da ke karkara, wani ƙarin ƙalubalen ne.

Ya yi nuni da cewa, duk da ƙalubalen da ake ci gaba da fuskanta a fanin, ya jaddada cewa; yin amfani da kayan aikin noma na zamani, na ƙara bunƙasa fannin a ƙasar, wanda kuma zai sanya a samu zuba jari na tsawon lokaci.

“Mai yiwuwa, yin amfani da kayan aikin noman na zamani, musamman na gajeren zango, ya kasance mai tsada, amma a dogon zango za a iya samun riba mai ɗimbin yawa,” a cewar shugaban.

Agbayewa ya ƙara da cewa, manoman da suka rungumi yin noma da kayan aikin na zamani, za su iya yin noma mai ɗimbin yawa tare da rage ɓata lokaci da kuma rage yin asara.

Ya ƙara da cewa, idan aka rungumi yin noma da kayan aikin na zmani, hakan zai ƙara taimakawa, wajen bunƙasa noma da rage ɗaukar hayar Leburori tare da kuma jawo ra’ayin matasan ƙasar, su rungumi fannin na aikin noma.

Agbayewa ya yi kira ga gwamnatin tarayya da na jihohi, da su samar da cibiyoyin bayar da hayar taraktocin noma, sannan kuma a kan farashi mai rahusa, musaman domin manoman ƙasar su riƙa yin haya, idan sun tashi yin noma.

Ya kuma yi kira da a ƙara samar da masana’antu, ƙera kayan aikin noma na zamani a ƙasar, musamman domin samar da kayan gyaransu, wanda hakan zai sanya a rage shigo da kayan zuwa cikin ƙasar, daga ƙetare.

A cewarsa, ƙara faɗaɗa samar da kayan aikin noma na zamani, zai ƙara taimakawa, wajen samar da wadataccen abinci a ƙaar tare da rage shigo da abinci daga ƙetare.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.