ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirkirar jami’an Tsaro na Jihohi Na Kara Yaɗuwar Makamai – Kwankwaso

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya danganta yaduwar makamai tsakanin ’yan Nijeriya da kafa ƙungiyoyin tsaro na jihohi. A cewar Kwankwaso, matsalar ta nuna cewa gwamnatin tarayya tana fama da fuskantar gazawar dakile ta.

A wata sanarwa da ya wallafa a X ranar Litinin, Kwankwaso ya ce: “Abubuwan da ke faruwa a ƙasarmu kwanan nan sun cika ni da damuwa matuƙa game da halin da harkokin ƙasa ke ciki.” Ya bayyana cewa, yayin da ɗaukar matakin dakile rashin tsaro ya rataya ne a wuyan gwamnatin tarayya, ya kamata a yi hakan tare da haɗin gwuiwar gwamnatocin jihohi, da kananan hukumomi, da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Kwankwaso Ya Tarɓi Gwamna Abba Yusuf A Abuja Bayan Kyautar NEAPS
  • APC Ba Ta Da Ƙarfin Da Za Ta Lashe Zaɓen 2027 Ba Tare Da Kwankwaso Ba – Dungurawa 

Kwankwaso ya kuma soki amincewar da aka bai wa jihohi su kafa ƙungiyoyin tsaro na sa-kai, inda ya ce: “Duk da cewa manufar tana da kyau, wannan mataki ya haifar da yaduwar makamai kanana ba tare da kulawa ba a fadin ƙasa.” Ya ƙara da gargadin cewa wasu mutane suna amfani da wannan damar wajen kafa rundunoni nasu, abin da ke ƙara barazana ga zaman lafiya a ƙasa.

ADVERTISEMENT

Tsohon Ministan Tsaron ya bayyana damuwarsa kan ƙara samun nuna bambanci bisa kabila da yanki, inda ake tsangwamar wasu mutane, da tsare su ba bisa ka’ida ba, ko kuma azabtar da su a wasu sassan ƙasar. Haka zalika, ya nuna yadda ƙara samun cin zarafi, da tsangwama da kuma maganganun ƙiyayya a kafafen sada zumunta ke ƙara ƙarfafa rigingimu na kabilanci da addini.

Jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa ya ce waɗannan abubuwa na barazana ga haɗin kai da zaman lafiya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin dakile waɗannan halaye kafin su ƙara zama babbar barazana, tare da nuna cewa yaduwar makamai a yanzu abin takaici ne kuma ba abin da za a yarda da shi ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Kwankwaso
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Rikicin Boko Haram Ya Daɗe Fiye da Yaƙin Basasar Najeriya – Obasanjo

Rikicin Boko Haram Ya Daɗe Fiye da Yaƙin Basasar Najeriya - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.