ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirkirar jami’an Tsaro na Jihohi Na Kara Yaɗuwar Makamai – Kwankwaso

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya danganta yaduwar makamai tsakanin ’yan Nijeriya da kafa ƙungiyoyin tsaro na jihohi. A cewar Kwankwaso, matsalar ta nuna cewa gwamnatin tarayya tana fama da fuskantar gazawar dakile ta.

A wata sanarwa da ya wallafa a X ranar Litinin, Kwankwaso ya ce: “Abubuwan da ke faruwa a ƙasarmu kwanan nan sun cika ni da damuwa matuƙa game da halin da harkokin ƙasa ke ciki.” Ya bayyana cewa, yayin da ɗaukar matakin dakile rashin tsaro ya rataya ne a wuyan gwamnatin tarayya, ya kamata a yi hakan tare da haɗin gwuiwar gwamnatocin jihohi, da kananan hukumomi, da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Kwankwaso Ya Tarɓi Gwamna Abba Yusuf A Abuja Bayan Kyautar NEAPS
  • APC Ba Ta Da Ƙarfin Da Za Ta Lashe Zaɓen 2027 Ba Tare Da Kwankwaso Ba – Dungurawa 

Kwankwaso ya kuma soki amincewar da aka bai wa jihohi su kafa ƙungiyoyin tsaro na sa-kai, inda ya ce: “Duk da cewa manufar tana da kyau, wannan mataki ya haifar da yaduwar makamai kanana ba tare da kulawa ba a fadin ƙasa.” Ya ƙara da gargadin cewa wasu mutane suna amfani da wannan damar wajen kafa rundunoni nasu, abin da ke ƙara barazana ga zaman lafiya a ƙasa.

ADVERTISEMENT

Tsohon Ministan Tsaron ya bayyana damuwarsa kan ƙara samun nuna bambanci bisa kabila da yanki, inda ake tsangwamar wasu mutane, da tsare su ba bisa ka’ida ba, ko kuma azabtar da su a wasu sassan ƙasar. Haka zalika, ya nuna yadda ƙara samun cin zarafi, da tsangwama da kuma maganganun ƙiyayya a kafafen sada zumunta ke ƙara ƙarfafa rigingimu na kabilanci da addini.

Jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa ya ce waɗannan abubuwa na barazana ga haɗin kai da zaman lafiya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin dakile waɗannan halaye kafin su ƙara zama babbar barazana, tare da nuna cewa yaduwar makamai a yanzu abin takaici ne kuma ba abin da za a yarda da shi ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Kwankwaso
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Rikicin Boko Haram Ya Daɗe Fiye da Yaƙin Basasar Najeriya – Obasanjo

Rikicin Boko Haram Ya Daɗe Fiye da Yaƙin Basasar Najeriya - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.