Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa yaki da ’yan Boko Haram a Nijeriya ya wuce tsawon Yaƙin Basasa na 1967–1970. Obasanjo ya yi wannan tsokaci ne ranar Lahadi a shirin Toyin Falola Interviews, wanda aka watsa kai tsaye a kafafen sada zumunta, inda Bishop Matthew Kukah da tsohon Mataimakin Gwamnan CBN, Kingsley Moghalu suka halarta.
Ya ce dakile ‘yan ta’adda na bukatar haɗin dabaru na musamman, da kayan aiki na zamani, da bayanai masu inganci, da fasahar zamani. Obasanjo ya ce babu laifi sojojin Nijeriya su samu horo daga ƙasashen da suka yi nasara wajen yaki da ‘yan ta’adda, inda ya kawo Colombia a matsayin misali. Ya jaddada cewa horon sojoji na yau da kullum ba ya isa wajen tunkarar ‘yan ta’adda da suke yawo ko shiga cikin jama’a.
- Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika
- Kuskure Ne Tattaunawa Da Ƴan Bindiga, Yafi Dacewa A Nemi Tallafin Ƙasashen Waje – Obasanjo
Obasanjo yayi gargadin cewa rashin kyakkyawar hanyar siyan kayan yaki da musayar bayanai zai iya kawo koma baya a yaki da ‘yan ta’adda, yana mai cewa bai kamata a bar sojoji su kadai su sayi kayan yaki ba, domin harkar ta zama kamar masana’antu. Daga kwarewarsa wajen yaki da masu tada zaune tsaye a Niger Delta, ya bayyana cewa ba za a iya kawar da yiwuwar haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da ‘yan ta’adda ba.
Tsohon shugaban ya ce: “Sai da yaƙin basasa ya ɗauki watanni 30, duk da cewa mun yi tsammanin zai ɗauki watanni shida. Amma wannan yaki da ‘yan ta’adda da masu laifi ya ɗauki kusan shekaru 15.” Obasanjo ya kara da cewa ya ziyarci Maiduguri a 2011 domin fahimtar asali, da koke-koke da tsarin shugabancin Boko Haram. Ya kuma bayyana cewa a farko ‘yan ta’addan sun ƙi tattaunawa da Gwamnatin Tarayya, kafin daga bisani su amince da tsagaita wuta na kwanaki 21, wanda bai yi tasiri ba saboda rashin kyakkyawar tattaunawa da shugabanninsu














