ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

by Rabi'u Ali Indabawa
14 minutes ago
Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya nuna damuwarsa kan yadda shanu ke yawo a titunan Abuja, yana mai bayyana lamarin a matsayin batun tsaron kasa.

Ministan ya jaddada cewa bai kamata a bar dabbobi suna yawo ba tare da kulawa a babban birnin kasar ba.

Wike ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin tattaunawarsa ta wata-wata da manema labarai a Abuja, lokacin da yake amsa tambayoyi kan karuwa da aka samu na shanu a wasu sassan birnin duk da kokarin da ake yi na inganta gine-gine da kyawun birnin.

ADVERTISEMENT

Da aka tambaye shi game da shanun da ke kiwo a filayen ciyawa da kuma yawo a kan tituna a Abuja, Wike ya ce: “Wannan batu ne da ya shafi tsaron kasa.”

Lokacin da aka kara matsa masa ya bayyana yadda lamarin ke da alaka da tsaron kasa, sai ya amsa da cewa: “A’a, a’a, a’a. Dole ne mu fuskanci gaskiya.”

LABARAI MASU NASABA

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

A cewarsa, manufar Gwamnatin Tarayya ta kiwon dabbobi a ruga (ranching) ita ce hanya mafi dacewa wajen magance matsalar.

“Daya daga cikin abubuwan da muka fara yi lokacin da muka zo shi ne bin umarnin Shugaban Kasa cewa mu aiwatar da tsarin kiwon dabbobi a ruga domin mu fitar da shanu da sauran dabbobi daga cikin birni,” in ji shi.

Yana bayyana halin da ake ciki a matsayin abin takaici, Wike ya kara da cewa:

“Abin na bata wa ido rai. Bai dace ba. Ba abu ne mai kyau ba.”

Ministan ya ce a kasashen da suka ci gaba ba a barin dabbobi suna yawo cikin birane.

“Muna da kasashe masu ci gaba da ke kiwon shanu. Sai dai idan ka je wuraren da ake kiwon su za ka gan su. Ka je Saudiyya. Ka je sauran manyan birane. Ba za ka ga shanu suna yawo a can ba,” in ji shi.

Wike ya kuma koka cewa duk lokacin da gwamnati ta fito da wasu manufofi domin magance irin wannan matsala, mutane kan yi musu mummunar fahimta ko kuma su mayar da lamarin siyasa.

“Da zarar ka fara aiwatar da wasu manufofi, mutane sai su ce wai ana yin hakan ne saboda wani dalili. A’a, a’a, a’a. Batu ne na tsaron kasa,” in ji shi.

Ministan ya kuma yi magana kan matsalar kasuwanci a kan tituna, bara da sauran abubuwan da ke kawo cikas a tsakiyar birnin.

A cewarsa, Hukumar Gudanarwar Babban Birnin Tarayya (FCTA) na ci gaba da kokarin korar ‘yan kasuwar da ke kasuwanci a bakin tituna da wuraren da ba a amince da su ba, amma tana bukatar karin goyon bayan jama’a domin ci gaba da nasarar wannan aiki.

“Idan ka ga an ware maka wuri don yin kasuwanci, to a can ya kamata ka yi. Ba wai ka zauna a ko’ina ba. Daga baya sai ka ga an mayar da wurin kasuwa alhali ba kasuwa ba ce. Wannan ma wani nau’in kawo cikas ne,” in ji shi.

Wike ya kara da cewa matakan da gwamnati ke dauka na da nufin kare martaba da kyawun babban birnin kasar.

“Mun dade muna wannan aiki kuma za mu ci gaba da yi. Amma muna bukatar goyon bayan kafofin yada labarai domin wayar da kan jama’a cewa abin da muke yi yana cikin muradun al’umma baki daya.

“Wannan shi ne babban birni guda daya da Nijeriya ke da shi. Ba za mu bari a lalata shi ba kawai saboda wani yana neman hanyar samun abin da zai ci yau da kullum. Neman abin rayuwa ba yana nufin a karya dokokin da aka kafa ba,” in ji ministan.

Wike
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara
Labarai

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
Labarai

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

June 5, 2026
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

June 5, 2026
Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

June 5, 2026
GORON JUMA’A 17-04-2026

Goron Juma’a

June 5, 2026
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

June 5, 2026
Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

June 5, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.