Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya nuna damuwarsa kan yadda shanu ke yawo a titunan Abuja, yana mai bayyana lamarin a matsayin batun tsaron kasa.
Ministan ya jaddada cewa bai kamata a bar dabbobi suna yawo ba tare da kulawa a babban birnin kasar ba.
Wike ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin tattaunawarsa ta wata-wata da manema labarai a Abuja, lokacin da yake amsa tambayoyi kan karuwa da aka samu na shanu a wasu sassan birnin duk da kokarin da ake yi na inganta gine-gine da kyawun birnin.
Da aka tambaye shi game da shanun da ke kiwo a filayen ciyawa da kuma yawo a kan tituna a Abuja, Wike ya ce: “Wannan batu ne da ya shafi tsaron kasa.”
Lokacin da aka kara matsa masa ya bayyana yadda lamarin ke da alaka da tsaron kasa, sai ya amsa da cewa: “A’a, a’a, a’a. Dole ne mu fuskanci gaskiya.”
A cewarsa, manufar Gwamnatin Tarayya ta kiwon dabbobi a ruga (ranching) ita ce hanya mafi dacewa wajen magance matsalar.
“Daya daga cikin abubuwan da muka fara yi lokacin da muka zo shi ne bin umarnin Shugaban Kasa cewa mu aiwatar da tsarin kiwon dabbobi a ruga domin mu fitar da shanu da sauran dabbobi daga cikin birni,” in ji shi.
Yana bayyana halin da ake ciki a matsayin abin takaici, Wike ya kara da cewa:
“Abin na bata wa ido rai. Bai dace ba. Ba abu ne mai kyau ba.”
Ministan ya ce a kasashen da suka ci gaba ba a barin dabbobi suna yawo cikin birane.
“Muna da kasashe masu ci gaba da ke kiwon shanu. Sai dai idan ka je wuraren da ake kiwon su za ka gan su. Ka je Saudiyya. Ka je sauran manyan birane. Ba za ka ga shanu suna yawo a can ba,” in ji shi.
Wike ya kuma koka cewa duk lokacin da gwamnati ta fito da wasu manufofi domin magance irin wannan matsala, mutane kan yi musu mummunar fahimta ko kuma su mayar da lamarin siyasa.
“Da zarar ka fara aiwatar da wasu manufofi, mutane sai su ce wai ana yin hakan ne saboda wani dalili. A’a, a’a, a’a. Batu ne na tsaron kasa,” in ji shi.
Ministan ya kuma yi magana kan matsalar kasuwanci a kan tituna, bara da sauran abubuwan da ke kawo cikas a tsakiyar birnin.
A cewarsa, Hukumar Gudanarwar Babban Birnin Tarayya (FCTA) na ci gaba da kokarin korar ‘yan kasuwar da ke kasuwanci a bakin tituna da wuraren da ba a amince da su ba, amma tana bukatar karin goyon bayan jama’a domin ci gaba da nasarar wannan aiki.
“Idan ka ga an ware maka wuri don yin kasuwanci, to a can ya kamata ka yi. Ba wai ka zauna a ko’ina ba. Daga baya sai ka ga an mayar da wurin kasuwa alhali ba kasuwa ba ce. Wannan ma wani nau’in kawo cikas ne,” in ji shi.
Wike ya kara da cewa matakan da gwamnati ke dauka na da nufin kare martaba da kyawun babban birnin kasar.
“Mun dade muna wannan aiki kuma za mu ci gaba da yi. Amma muna bukatar goyon bayan kafofin yada labarai domin wayar da kan jama’a cewa abin da muke yi yana cikin muradun al’umma baki daya.
“Wannan shi ne babban birni guda daya da Nijeriya ke da shi. Ba za mu bari a lalata shi ba kawai saboda wani yana neman hanyar samun abin da zai ci yau da kullum. Neman abin rayuwa ba yana nufin a karya dokokin da aka kafa ba,” in ji ministan.














Discussion about this post