ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Wadannan Abubuwan Game Da Mazajenku?

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Bilkisu Tijjani Kasim

Yau tsaraba ce ga mata kan abubuwan da ya dace su sani game da mazajensu na aure.

Da farko kafin mu yi nisa, ya kamata mace ta yarda mijinta shi ne shugaba a kanta (wannan wajibi ne ba zabi ba), ko da kuwa ta girme shi da shekaru, ko ta fi shi kudi, ko ilimi, ko matsayi, ko karfi ko dai wani abu na rayuwa. Ki tuna fa shi ne ya je har gidanku ya nuna sha’awar kasancewa tare da ke na tsawon wani lokaci da ba shi da karshe sai fa in mutuwa ta zo.

Shi ne yake da hakkin kula da ke dangane da ci, sha, tufafi, matsuguni da kuma biya miki sauran bukatun rayuwa da babu wanda ya isa ya biya miki ban da shi.

ADVERTISEMENT

Akwai abubuwa da dama wadanda mata ya kamata su sani game da mazajensu, ga kadan daga cikin su kamar haka:

Yin kasa da sauti in kina magana da shi: Mace ta gari ita ce wacce ba ta daga muryarta idan tana magana da mijinta, ko da kuwa ranta ya baci. Yin hakan zai iya fusata shi kuma ta yiwu ma har ya yi abin da bai kamata ba. Idon kika fahimci cewa ya hau sama wato ransa ya baci, sai ke kuma ki sauko kasa.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

Ki ba shi hakuri in kin yi masa laifi: Dole ne mace in ta yi laifi ta bada hakuri. Wasu matan in sun yi laifin ma aka fada musu sai su fara musu, suna kokarin kare kansu. Mace ta gari ita ce wacce in ta yi laifi za ta yarda ta yi kuma ta bada hakuri.

Daukar shawararsa: Idan mijin ki ya baki shawara a kan wani abu ya kamata ki girmama ra’ayinsa in har bai ci karo da addini ba. Wannan shi zai tabbatar masa da cewa kina girmama shi.

Wannan yana da matukar muhimmanci. Wasu matan kafarsu kamar tana kaikayi, miji yana fita za su dauki gyale sai gidan makota ko gidan kawaye. Gaskiya hakan ba hali ne na gari ba.

Ki sani dole ne in za kika fita, ki fita da izinin mijinki, kuma wajibi ne ki tsaya a iya inda kika ce za ki je. Wasu matan za su tambayi izinin zuwa gida daya ko biyu, amma za su iya shiga gidaje goma.

Idon kina fita aiki, ya kamata ki kiyaye kanki daga abokan aikinki, ki rike amanar mijinki a wurin da baya nan. Wasu mazajen sun amince wa matansu amma su matan za su iya cin amanarsu.

Ki sani fa wasu mazan za su rinka kula ki ko da kuwa sun san kin yi aure kuma sun san mijin naki, musamman ma in kina da kyau kuma ke fara ce, kin san mafi yawan maza suna son farar mace har ma za ki ji wasu suna cewa “fara ko ‘yar gidan sarkin mayu ce”. Dole ki lura da irin wadannan domin komai kamun kanki sun san yadda za su shawo kanki domin ki kula su.

Su ma matan da suke fita aiki, ku ji tsoron Allah in kun fita daga gida kar ku tsaya ko ina sai wajen aikinku, haka kuma in kun dawo kar ku tsaya a ko ina sai gidanku. Wasu matan suna amfani da aikinsu sai su shiga kasuwanni su yi ta yawo da sunan sayayya suka je, gaskiya hakan ba shi da kyau.

Ki tuna fa ‘ya’yanki in sun dawo daga makaranta suna bukatar ganinki, haka kuma mijinki ma in da wuri yake dawowa daga wajen aikinsa yana bukatar ganin ki tare da kulawa daga wajenki.

Ya kamata mata su tuna cewa aure Ibadar Allah ce, yana da kyau su kyautata wajen zamantakewa da miji.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Next Post
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.