ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin CBN Kan Farfado Da Noman Kwakwar Manja Don Samar Wa Nijeriya Kudaden Musaya

by Abubakar Abba
4 years ago
CBN

Haramta shiga da manja da dangoginsa da kasar Indonesiya ta yi zuwa cikin kasar, musamman ganin cewa, kasar ce ke kan gaba a duniya wajen samar da shi, matakin nata ya zama wajibi ya zama darasi ga masu zuba jari a fannin da kuma yadda Nijeriya ke hankoron fitar da nata Manjan zuwa kasuwar duniya.

Kafin wannan matakin na haramtawar da kuma Manjan da aka sarrafa shi, Manjan ya kasance a kan gaba wajen samarwa Asiya kudaden musaya na kasar waje.

  • Yadda Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Suka Habaka Noma A Nijeriya

A watan Afirilun 2020, tan dinsa na samar wa da Indonesiya kimanin Dala 545, inda bayan shekaru biyu,ya haura zuwa Dala 1,700.Akasarin masana a fannin aikin noma sun bayyana takaicinsu, musamman duba a Jamhuriya ta daya ne, Asiya a karonta na farko ta zo Nijeriya ta dauki irin na kwakwar manja, amma abin takaici, a yau Indonesiya ta yi wa Nijeriya fintinkau wajen noman kwakwar manja da sarrafa ta.

ADVERTISEMENT

Sai dai, Nijeriya ganin irin mahimmancin da fannin noma yake da shi, ta samar da tsari don kara habaka fannin, musamman don kara bunkasa nomanta domin kara bunkasa tattalin kasar da kuma kara samarwa da kanta kudaden shiga na waje.

Misali, duba ga wannan fashin baki da aka zayyano, idan aka yi dubi a kan tsarin da Babban Bankin Nijeriya CBN ya kirkiro da tsarin don a farfado da fannin abu ne da za a iya cewa Nijeriya ta farga.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Tabbas, a kasuwar duniya ana bukatar ta matuka, masana na gamin cewa, an fi samun riba mai yawa a fannin fiye da a fannin samar da manfetur da iskar gas.

A bayyana ne yake a yanzu gangar manja ta fi ta gangar danyen mai tsada.Ana yin nomanta ne na dogon zango saboda tsawon. tsawon lokacin da take zauka kafin ta kammala girma, sabanin sauran amfanin gona.

Saboda haka ne mahukunta na yanzu a CBN suka yunkuro don su sake dawo martabar fannin a matsayin wanda za a iya amfani da shi, don a kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Bugu da kari, CBN ya zabo fannin a matsayin daya daga cikin fanonin da zai amfana da daukin tsarin da ya kirkiro da shi.

Ya na da kyau a sani cewa, kafin Nijeriya ta samu ‘yancin kanta daga gun Turawar muljin mallaka, noman Kwakwar ya taka muhimiyyar rawa wajen bunkasa tattalin arzikin Yammacin kasar nan.

An kiyasta cewa, gibin da ake da shi, na manja ya kai mitrik tan 1,250,000 inda kuma bukatar da ake da ita ta man a cikin kasar nan ta kai ta kimanin metirik tan 2,500,000 wanda kuma a kasar, ana noma metirik tan 1,250,000 kacal.

Har ila yau, CBN ya kuma mayar da hankali wajen sake farfado da fannin ta hanyar zuba kudade da samar da kayan aiki a Kudancin Nijeriya, musamman a Kudu Maso Gabas.

Daukin na CBN a fannin an yi ne don a kara yawan noman Kwakwar Manja
daga metirikw tan 1,250,000 zuwa metirik tan 2,500,000 nan da 2028 ta hanyar noma akalla, kadada 350,000 Babbar manufar da ake son cim ma a fannin shi ne, a samar da wadataccen manjan da dangoginsa a kasar nan tare da kuma samar da ingantaccen sa, kara samar da kudaden shiga ga Asusun ajiya na kasar da ke a ketare.

Kara bunkasa kwarewa dabarun noman Kwakwar Manja ‘yan Nijeriya, samarwa wadanda ke a fannin saukin samun rancen kudaden, samar da tallafi ga manya kananan sana’io domin a kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

A yanzu haka, ana kan tartaunawa da wasu jihohin da fannin ya durkushe a jihohin su kamar aikin na noman Kwakwar Manja da ake kira da Adapalm da ke a Kudu maso gabas tare da nemo masu ruwa da tsaki a fannin, inda ya zuwa yanzu, an kebe kadada 170,000 ga masu son zuba jari a jihohi 11.

Misali, Godwin Emefiele a 2019 ya kaddamar da shirin nomanta na (ESOPP), wanda yake ci gaba da fadada, inda a yanzu gwamnatin jihar ta kebe jimlar kadada 65,000 ga masu son zuba jarinsu a fannin.

Hakazalika, CBN ya zuba naira biliyan 51.29 a cikin ayyukan a jihar, inda kuma jihar ta Ondo ta kaddamar da ayyukin da ta yiwa lakabi da Red Gold Project.

Bugu da kari, jihar ta kuma kebe filin yin nomanta ga kamfani tare da tallafawa kananan manoman na Kwakwar Manja da ya kai jimlar kadada 54,000, musamman domin a noma jimlar kadada 6,000,inda tuni, manomanta suka Har ila yau, sauran jihohin na ci gaba da tattaunawa da CBN ta hanyar bankunan su ma ajiya wato na (DMBs), musamman domin a taimaka wa kananan manoman da ke a cikin fannin.

Tuni dai, wadanda ke Sa idok a fannin suka fara yin hasashen cewa, a 2022 da kuma bayanta, ana sa ran za a noma kadada 350,000 wacce kuma za a noma su a 2028.

Tun bayan da CBN ya kirkiro da tsarin, ya amince tare da kuma turawa manya, matsakaita da kanana a fannin naira biliyan 73.38 .

Yana zama dole a sanar da cewa, kara cigaban da Indonesiya ke samu a fannin ne ya kara bai wa Emefiele kwarin gwiwar yunkuri sake farfado da fannin a kasarnankwararru sun kuma yi kira ga masu son zuba jari a fannin a kasar nan kar su bari wannan damar ta kubuce masu, musamman ganin cewa, alfanun da za a samu, bai sa iyakaBanda wannan bangaren na noman kwakwar manja, akwai kuma yunkurin da ake yi don a kara habaka fannin aikin Man Gyada a kasar nan.

Amadi Manomin kwakwar manja ne da ke zaune a garin Owerri.

CBN
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Yusuf Buba Yakub Ya Yaba Da Matakan Da Kasar Sin Ta Dauka Na Taimaka Wa Afirka

Yusuf Buba Yakub Ya Yaba Da Matakan Da Kasar Sin Ta Dauka Na Taimaka Wa Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.