ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

by Leadership Hausa
7 months ago

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ƙaryata iƙirarin da ke alakanta shi da yiwuwar tikitin mataimakin shugaban ƙasa yak nema tare da tsohon mataimakin shugaba ƙasa, Atiku Abubakar a zaɓen 2027.

Ya ce shi kujerar shugaban ƙasar Nijeriya yake da buri kuma ba zai yi wa kowa mataimakin takara ba a zaɓen 2027.

  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Dakta Soky  Amachree: Dan Kishin Kasa Jakada Nagari

Kalamun Amaechi ya biyo bayan maganganun da abokin Atiku, Dele Momodu, wanda ya nuna cewa Atiku na iya la’akari da tsohon gwamnan Jihar Ribas a matsayin mataimakin takararsa idan Peter Obi ya ƙi haɗewa da shi.

ADVERTISEMENT

A cikin wata hira da ya yi da ƴan jarida, Momodu ya yaba tasirin siyasar Amaechi, yana bayyana shi a matsayin babban mutum da ya taimaka wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari har ya samu nasara a 2015.

Da yake bayar da martani ta bakin mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, Xavid Iyofor, Amaechi ya yi watsi da duk wata tattaunawa kan haɗin gwiwa da nufin sanya shi mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa. Iyofor ya bayyana cewa Amaechi na ganin lokaci ya yi da yankinn kuduncin Nijeriya zai sake samar da shugaban ƙasa na gaba, don haka ya fara neman tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Ya ce, “Amaechi ba ya neman zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa ga kowa. Bai yi niyyar zama mataimakin shugaban ƙasa ga kowa ba kuma ba zai yi ba.

”Amaechi bai sanin da wannan ba, kuma ba zai shiga kowane tattaunawa ba don ya zama mataimakin wani ɗan takarar shugaban ƙasa ba. Ko shakka babu Amaechi na neman zama shugaban Nijeriya ne ba wai don ya zama mataimakin wani ba.

“Ina shawartar ‘yan siyasa su bar kiran sunan Amaechi a wajen kowace tattaunawa kan wanda zai zama abokin takarar shugaban ƙasa,” in ji Iyofor.

Wannan ba shi ne karo na farko da Amaechi ya bayyana a niyyarsa a fili ba ta neman tikitin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC ba. A watan Agusta, ya yi alƙawarin cewa ba zai iya januewa kowane ɗan takara ba yayin zaɓen fid da gwani na jam’iyyar, yana mai jaddada cewa mutane ne ya kamata su yanke shawara kan wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

A farkon watan Yuli, ya kuma bayyana cewa shirye yake na yin wa’adi guda na shugaban ƙasa don inganta tsarin karɓa-karɓa da samun kwanciyar hankali na siyasa idan aka zaɓe shi a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

“Da ba don saboda yarjejeniyara ba, amsar ko zan tsaya takara a matsayin shugaban ƙasa zai kasance eh ne kai tsaye.

“Amma mene ne muka amince da shi? Kowa ya ajiye burinsa. Barinmu shi ne fara samun jam’iyya. Barinmu mu gina jam’iyyar kafin a fara batu kan shugabancin ƙasa,” in ji shi.

Amaechi ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC a shekarar 2022, inda ya zo na biyu bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu, wanda ya lashe tikitin jam’iyyar a wancan lokaci.

Shugaban
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.