Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ƙaryata iƙirarin da ke alakanta shi da yiwuwar tikitin mataimakin shugaban ƙasa yak nema tare da tsohon mataimakin shugaba ƙasa, Atiku Abubakar a zaɓen 2027.
Ya ce shi kujerar shugaban ƙasar Nijeriya yake da buri kuma ba zai yi wa kowa mataimakin takara ba a zaɓen 2027.
- Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
- Dakta Soky Amachree: Dan Kishin Kasa Jakada Nagari
Kalamun Amaechi ya biyo bayan maganganun da abokin Atiku, Dele Momodu, wanda ya nuna cewa Atiku na iya la’akari da tsohon gwamnan Jihar Ribas a matsayin mataimakin takararsa idan Peter Obi ya ƙi haɗewa da shi.
A cikin wata hira da ya yi da ƴan jarida, Momodu ya yaba tasirin siyasar Amaechi, yana bayyana shi a matsayin babban mutum da ya taimaka wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari har ya samu nasara a 2015.
Da yake bayar da martani ta bakin mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, Xavid Iyofor, Amaechi ya yi watsi da duk wata tattaunawa kan haɗin gwiwa da nufin sanya shi mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa. Iyofor ya bayyana cewa Amaechi na ganin lokaci ya yi da yankinn kuduncin Nijeriya zai sake samar da shugaban ƙasa na gaba, don haka ya fara neman tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.
Ya ce, “Amaechi ba ya neman zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa ga kowa. Bai yi niyyar zama mataimakin shugaban ƙasa ga kowa ba kuma ba zai yi ba.
”Amaechi bai sanin da wannan ba, kuma ba zai shiga kowane tattaunawa ba don ya zama mataimakin wani ɗan takarar shugaban ƙasa ba. Ko shakka babu Amaechi na neman zama shugaban Nijeriya ne ba wai don ya zama mataimakin wani ba.
“Ina shawartar ‘yan siyasa su bar kiran sunan Amaechi a wajen kowace tattaunawa kan wanda zai zama abokin takarar shugaban ƙasa,” in ji Iyofor.
Wannan ba shi ne karo na farko da Amaechi ya bayyana a niyyarsa a fili ba ta neman tikitin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC ba. A watan Agusta, ya yi alƙawarin cewa ba zai iya januewa kowane ɗan takara ba yayin zaɓen fid da gwani na jam’iyyar, yana mai jaddada cewa mutane ne ya kamata su yanke shawara kan wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.
A farkon watan Yuli, ya kuma bayyana cewa shirye yake na yin wa’adi guda na shugaban ƙasa don inganta tsarin karɓa-karɓa da samun kwanciyar hankali na siyasa idan aka zaɓe shi a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.
“Da ba don saboda yarjejeniyara ba, amsar ko zan tsaya takara a matsayin shugaban ƙasa zai kasance eh ne kai tsaye.
“Amma mene ne muka amince da shi? Kowa ya ajiye burinsa. Barinmu shi ne fara samun jam’iyya. Barinmu mu gina jam’iyyar kafin a fara batu kan shugabancin ƙasa,” in ji shi.
Amaechi ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC a shekarar 2022, inda ya zo na biyu bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu, wanda ya lashe tikitin jam’iyyar a wancan lokaci.













