ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

by Leadership Hausa
7 months ago

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ƙaryata iƙirarin da ke alakanta shi da yiwuwar tikitin mataimakin shugaban ƙasa yak nema tare da tsohon mataimakin shugaba ƙasa, Atiku Abubakar a zaɓen 2027.

Ya ce shi kujerar shugaban ƙasar Nijeriya yake da buri kuma ba zai yi wa kowa mataimakin takara ba a zaɓen 2027.

  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Dakta Soky  Amachree: Dan Kishin Kasa Jakada Nagari

Kalamun Amaechi ya biyo bayan maganganun da abokin Atiku, Dele Momodu, wanda ya nuna cewa Atiku na iya la’akari da tsohon gwamnan Jihar Ribas a matsayin mataimakin takararsa idan Peter Obi ya ƙi haɗewa da shi.

ADVERTISEMENT

A cikin wata hira da ya yi da ƴan jarida, Momodu ya yaba tasirin siyasar Amaechi, yana bayyana shi a matsayin babban mutum da ya taimaka wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari har ya samu nasara a 2015.

Da yake bayar da martani ta bakin mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, Xavid Iyofor, Amaechi ya yi watsi da duk wata tattaunawa kan haɗin gwiwa da nufin sanya shi mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa. Iyofor ya bayyana cewa Amaechi na ganin lokaci ya yi da yankinn kuduncin Nijeriya zai sake samar da shugaban ƙasa na gaba, don haka ya fara neman tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Ya ce, “Amaechi ba ya neman zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa ga kowa. Bai yi niyyar zama mataimakin shugaban ƙasa ga kowa ba kuma ba zai yi ba.

”Amaechi bai sanin da wannan ba, kuma ba zai shiga kowane tattaunawa ba don ya zama mataimakin wani ɗan takarar shugaban ƙasa ba. Ko shakka babu Amaechi na neman zama shugaban Nijeriya ne ba wai don ya zama mataimakin wani ba.

“Ina shawartar ‘yan siyasa su bar kiran sunan Amaechi a wajen kowace tattaunawa kan wanda zai zama abokin takarar shugaban ƙasa,” in ji Iyofor.

Wannan ba shi ne karo na farko da Amaechi ya bayyana a niyyarsa a fili ba ta neman tikitin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC ba. A watan Agusta, ya yi alƙawarin cewa ba zai iya januewa kowane ɗan takara ba yayin zaɓen fid da gwani na jam’iyyar, yana mai jaddada cewa mutane ne ya kamata su yanke shawara kan wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

A farkon watan Yuli, ya kuma bayyana cewa shirye yake na yin wa’adi guda na shugaban ƙasa don inganta tsarin karɓa-karɓa da samun kwanciyar hankali na siyasa idan aka zaɓe shi a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

“Da ba don saboda yarjejeniyara ba, amsar ko zan tsaya takara a matsayin shugaban ƙasa zai kasance eh ne kai tsaye.

“Amma mene ne muka amince da shi? Kowa ya ajiye burinsa. Barinmu shi ne fara samun jam’iyya. Barinmu mu gina jam’iyyar kafin a fara batu kan shugabancin ƙasa,” in ji shi.

Amaechi ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC a shekarar 2022, inda ya zo na biyu bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu, wanda ya lashe tikitin jam’iyyar a wancan lokaci.

Shugaban
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.