ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kujerar Shugaban Ƙasa Nake Buƙata A 2027 Ba Mataimaki Ba – Amaechi

by Leadership Hausa
6 months ago

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ƙaryata iƙirarin da ke alakanta shi da yiwuwar tikitin mataimakin shugaban ƙasa yak nema tare da tsohon mataimakin shugaba ƙasa, Atiku Abubakar a zaɓen 2027.

Ya ce shi kujerar shugaban ƙasar Nijeriya yake da buri kuma ba zai yi wa kowa mataimakin takara ba a zaɓen 2027.

  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Dakta Soky  Amachree: Dan Kishin Kasa Jakada Nagari

Kalamun Amaechi ya biyo bayan maganganun da abokin Atiku, Dele Momodu, wanda ya nuna cewa Atiku na iya la’akari da tsohon gwamnan Jihar Ribas a matsayin mataimakin takararsa idan Peter Obi ya ƙi haɗewa da shi.

ADVERTISEMENT

A cikin wata hira da ya yi da ƴan jarida, Momodu ya yaba tasirin siyasar Amaechi, yana bayyana shi a matsayin babban mutum da ya taimaka wa tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari har ya samu nasara a 2015.

Da yake bayar da martani ta bakin mai taimaka masa kan harkokin watsa labarai, Xavid Iyofor, Amaechi ya yi watsi da duk wata tattaunawa kan haɗin gwiwa da nufin sanya shi mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa. Iyofor ya bayyana cewa Amaechi na ganin lokaci ya yi da yankinn kuduncin Nijeriya zai sake samar da shugaban ƙasa na gaba, don haka ya fara neman tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Ya ce, “Amaechi ba ya neman zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa ga kowa. Bai yi niyyar zama mataimakin shugaban ƙasa ga kowa ba kuma ba zai yi ba.

”Amaechi bai sanin da wannan ba, kuma ba zai shiga kowane tattaunawa ba don ya zama mataimakin wani ɗan takarar shugaban ƙasa ba. Ko shakka babu Amaechi na neman zama shugaban Nijeriya ne ba wai don ya zama mataimakin wani ba.

“Ina shawartar ‘yan siyasa su bar kiran sunan Amaechi a wajen kowace tattaunawa kan wanda zai zama abokin takarar shugaban ƙasa,” in ji Iyofor.

Wannan ba shi ne karo na farko da Amaechi ya bayyana a niyyarsa a fili ba ta neman tikitin takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC ba. A watan Agusta, ya yi alƙawarin cewa ba zai iya januewa kowane ɗan takara ba yayin zaɓen fid da gwani na jam’iyyar, yana mai jaddada cewa mutane ne ya kamata su yanke shawara kan wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

A farkon watan Yuli, ya kuma bayyana cewa shirye yake na yin wa’adi guda na shugaban ƙasa don inganta tsarin karɓa-karɓa da samun kwanciyar hankali na siyasa idan aka zaɓe shi a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.

“Da ba don saboda yarjejeniyara ba, amsar ko zan tsaya takara a matsayin shugaban ƙasa zai kasance eh ne kai tsaye.

“Amma mene ne muka amince da shi? Kowa ya ajiye burinsa. Barinmu shi ne fara samun jam’iyya. Barinmu mu gina jam’iyyar kafin a fara batu kan shugabancin ƙasa,” in ji shi.

Amaechi ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC a shekarar 2022, inda ya zo na biyu bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu, wanda ya lashe tikitin jam’iyyar a wancan lokaci.

Shugaban
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.