Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, Operation Hadin Kai, sun kama wani matashi mai shekaru 15 da ake zargi da hannu a harin da ya yi sanadiyyar mutuwar wani babban jami’in soja a jihar Borno.
An kama wanda ake zargin, Tijjani, ne a Ngamdu yayin da ake zargin yana kan hanyarsa ta sayen abinci ga ‘yan ƙungiyar. Majiyoyin soji sun alaƙanta shi da harin da ya kashe Oseni Braimah tare da wasu sojoji uku, bayan farmakin da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai kan sansanin soja.
- ADC Ta Nuna Aniyar Kwace Borno A Shugabancin Ƙasa A 2027, Ta Soki Bola Tinubu
- INEC Na Yunƙurin Hana Mu Fitar Da Ƴan Takara – ADC
A cikin wani bidiyo da ke yawo, matashin ya amince da shiga wasu hare-hare a Benisheik da Ngamdu, yana mai cewa sun fito ne daga Jilli inda suke komawa bayan kowane hari. Ya kuma bayyana cewa an aiko shi da kuɗi N850,000 domin ɗauko kayayyaki kafin a kama shi.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan kama wanda ake zargin.















Discussion about this post