ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya

by yahuzajere
3 years ago
NIS

A shirye-shiryen taron masu ruwa da tsaki da take shirin gudanarwa, Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) reshen Jihar Ribas, ta nemi a karfafa bunkasa kwazon bil’adama ga kwararrun ‘yan Nijeriya masu zaman kansu da ke aiki a bangaren tattalin arziki na Kamfanoni, Kungiyoyi don kawo ci gaban fasaha bisa tanadin gwamnati a tsarin tallafin da ‘yan kasashen waje da kamfanoni ke bayarwa.

Hukumar ta nemi a rika keɓe kaso na musamman don bai wa ɗaliban Nijeriya damar haɓaka ƙwarewar ɗan’adam a kan aiki don ba da damar samun nasarar koyon fasahar aiki kamar yadda aka tsara da kuma sanya su a cikin tanadin Tallafin Kirkiro da Fasaha. Inda hukumar ta NIS ta kara da cewa yawancin ƙwararrun ‘yan Nijeriya ba su samun damar haɓaka kwazon aiki cikin hikima da ɗaukar nauyinsu kamar yadda aka tsara.

Don haka, NIS reshen Jihar Ribas bisa jagorancin Kwanturola Sunday James, ta yunkura domin ganin alakar da ake da da kamfanoni a Jihar Ribas, ya kara zama mai muhimmanci domin ci gaban al’umma, da kawar da takaici da kuma guje wa tabarbarewar kwakwalwa sakamakon rashin gamsuwa da kwazon aiki da kawo wa bangaren sana’o’i ci gaba a cikin gida.

ADVERTISEMENT
  • NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James
  • Ma’aikatar Hukumar Shige Da Fice Ta Nijeriya Na Gayyatar Jarabawar Daukar Aiki

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas, James Sunday, kamar yadda wata sanarwar manema labarai daga reshen hukumar ta nunar, yana da ra’ayin cewa ya kamata ’yan Nijeriya da suka cancanta su ci gajiyar aikinsu a cikin gida, ka da ya zama ‘yan kasar waje na amfani da su ne kawai sannan idan sun gama su tsere zuwa kasashensu na asali tare da barin ‘yan kasa da neman ayyuka masu gwabi a ketare.

A ganin Kwanturolan, ayyukan da ake bai wa ’yan Nijeriya sai ya zama dan kasar waje yake kula da su, idan dan kasar wajen ne ya fi saninsa, domin a samu damar koyar da ‘yan kasa fasahar wanda shi ne dalili na farko na sashen shirin dalibai a cikin tsarin Tallafin ‘Yan Kasar Waje da Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta amince da shi kuma Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya ta aiwatar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa reshen Jihar Ribas na karfafa gwiwar masana’antu, kamfanoni da kungiyoyi masu zaman kansu na tattalin arzikin kasa da kuma sauran hukumomin bangaren gwamnati da su hada kai da Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya don bai wa ’yan Nijeriya ƙwararru damar kara inganta kwarewarsu ta sanin makamar aiki.

Ta kara da cewa, domin samar da kyakykyawan aiki na ilimi da samar da aikin yi, dole ne a yaki matsalar tabarbarewar kwakwalwa musamman ga kwararrun ‘yan Nijeriya da ke da aikin yi don karfafa ingantaccen ilimi da ilmantarwa maimakon ba da shaidar karatu kawai, “Shawarar hakan tana cikin shirye-shiryen taron wayar da kan masu ruwa da tsaki a jihar ta Ribas.” In ji NIS reshen jihar.

 

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.