ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya

by yahuzajere
3 years ago
NIS

A shirye-shiryen taron masu ruwa da tsaki da take shirin gudanarwa, Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) reshen Jihar Ribas, ta nemi a karfafa bunkasa kwazon bil’adama ga kwararrun ‘yan Nijeriya masu zaman kansu da ke aiki a bangaren tattalin arziki na Kamfanoni, Kungiyoyi don kawo ci gaban fasaha bisa tanadin gwamnati a tsarin tallafin da ‘yan kasashen waje da kamfanoni ke bayarwa.

Hukumar ta nemi a rika keɓe kaso na musamman don bai wa ɗaliban Nijeriya damar haɓaka ƙwarewar ɗan’adam a kan aiki don ba da damar samun nasarar koyon fasahar aiki kamar yadda aka tsara da kuma sanya su a cikin tanadin Tallafin Kirkiro da Fasaha. Inda hukumar ta NIS ta kara da cewa yawancin ƙwararrun ‘yan Nijeriya ba su samun damar haɓaka kwazon aiki cikin hikima da ɗaukar nauyinsu kamar yadda aka tsara.

Don haka, NIS reshen Jihar Ribas bisa jagorancin Kwanturola Sunday James, ta yunkura domin ganin alakar da ake da da kamfanoni a Jihar Ribas, ya kara zama mai muhimmanci domin ci gaban al’umma, da kawar da takaici da kuma guje wa tabarbarewar kwakwalwa sakamakon rashin gamsuwa da kwazon aiki da kawo wa bangaren sana’o’i ci gaba a cikin gida.

ADVERTISEMENT
  • NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James
  • Ma’aikatar Hukumar Shige Da Fice Ta Nijeriya Na Gayyatar Jarabawar Daukar Aiki

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Jihar Ribas, James Sunday, kamar yadda wata sanarwar manema labarai daga reshen hukumar ta nunar, yana da ra’ayin cewa ya kamata ’yan Nijeriya da suka cancanta su ci gajiyar aikinsu a cikin gida, ka da ya zama ‘yan kasar waje na amfani da su ne kawai sannan idan sun gama su tsere zuwa kasashensu na asali tare da barin ‘yan kasa da neman ayyuka masu gwabi a ketare.

A ganin Kwanturolan, ayyukan da ake bai wa ’yan Nijeriya sai ya zama dan kasar waje yake kula da su, idan dan kasar wajen ne ya fi saninsa, domin a samu damar koyar da ‘yan kasa fasahar wanda shi ne dalili na farko na sashen shirin dalibai a cikin tsarin Tallafin ‘Yan Kasar Waje da Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta amince da shi kuma Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya ta aiwatar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa reshen Jihar Ribas na karfafa gwiwar masana’antu, kamfanoni da kungiyoyi masu zaman kansu na tattalin arzikin kasa da kuma sauran hukumomin bangaren gwamnati da su hada kai da Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya don bai wa ’yan Nijeriya ƙwararru damar kara inganta kwarewarsu ta sanin makamar aiki.

Ta kara da cewa, domin samar da kyakykyawan aiki na ilimi da samar da aikin yi, dole ne a yaki matsalar tabarbarewar kwakwalwa musamman ga kwararrun ‘yan Nijeriya da ke da aikin yi don karfafa ingantaccen ilimi da ilmantarwa maimakon ba da shaidar karatu kawai, “Shawarar hakan tana cikin shirye-shiryen taron wayar da kan masu ruwa da tsaki a jihar ta Ribas.” In ji NIS reshen jihar.

 

NIS
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

Bai Kamata A Ba Emefiele Hutun Zuwa Karo Karatu Ba –Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.