Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa shiyyar Arewa, Sanata Abubakar Kyari, ya zama shugaban rikon jam’iyyar APC na kasa.
Hakan ya biyo bayan murabus din da Sanata Abdullahi Adamu ya yi a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.
- Abdullahi Adamu Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa
- Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo
Kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanada, idan shugaban jam’iyyar na kasa ya yi murabus, mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa daga shiyya ne zai karbi ragamar mulki.
Kyari ya jagoranci wasu mambobin kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) zuwa wani taro da ke gudanarwa a halin yanzu a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja cikin tsauraran matakan tsaro.
Wadanda suka shiga taron da Kyari sun hada da Mataimakin Shugaban Kasa Jam’iyyar daga yankin Kudu, Emma Enukwu da takwaransa na yankin Arewa Maso Yamma, Salihu Lukman da Kuma Mataimakin Shugaban Kasa na shiyyar Arewa Maso Gabas, Salihu Mustapha da takwaransa na Arewa Ta Tsakiya, Muazu BawaBawa da Mataimakin shugaban na Kudu maso Yamma, Issacs Kekemeke da Mataimakin shugaban na kudu maso gabas , Ejoroma Arodiogu da mataimakin sakataren Jam’iyyar na kasa, Barr. Festus Fuanter.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp