ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
Alkama

Manoman rani na Alkama a Jihar Kano, na ci gaba da kokawa, kan gazawar gwamnatin tarayya, na cika alkawarinta na samar musu da dauki a karkashin shirinta na aikin noma na NAGS-AP.

A cewarsu, sun jira samun daukin daga wurin gwamnati, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da nanata alkawarin da gwamnatin ta yi.

  • Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata – Shehu Sani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Har ila yau, sun koka da cewa; gwamnatin ta sha yi musu alkawarin samar musu dauki, musamman wajen samar musu da kayan aiki a cikin rahusa, amma har zuwa yanzu, ba su gani a kas ba.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikinsu, Malam Habibu Garba da ke yin noma a Karamar Hukumar Garun Malam a jihar, ya sanar da cewa; jiran nasu ya ci gaba da kasancewa tamkar jiran gawon-shanu, na samu dauki daga wurin gwamnatin.

Gwamnatin, ta dai tsara shirin na NAGS-AP, da nufin kara bunkasa noman Alkama a cikin kasar, musamman domin a rage dogaro da shigo da ita daga ketare da kuma kara karfafa nomanta a fadin kasar baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Sai dai, abin takaici, bayan shafe watanni manoman nata na jiran daukin, amma shiru kake ji, ganin cewa; ba su samu ba har aka fara gudanar da kakar noman rani na 2026.

Rahotannin sun bayyana cewa, daukin da aka tsara za a samarwa da manoman Alkamar, ya hada da rage musu farashin kayan nomanta da samar musu da ingantaccen takin zamani, da za a iya yin amfani da su, hekta guda 3,000 da aka kiyasata.

Kazalika, an tsara cewa; kowanne manominta daya zai samu buhu mai nauyin kilo 50, na ingantaccen irin noma da buhu uku na takin zamani, kan farashin gwamnati na kashi 50.

Sai dai, wani daga cikin manoman Alkamar a jihar, Shehu Bello Bahago ya ce; shigar da manoman suka yi a cikin shirin gwamnati wasu kakar noma na baya sun amfana.

Ya yi gargadin cewa, matukar gwamnatin ta gaza cika alkawarin, hakan zai iya janyo wa manoman jihar, su gaza ci gaba da nomanta.

“Manomanta da dama, sun zuba jarinsu a kakar nomanta ta bana, musamman ganin cewa; akasarinsu sun dogara ne da daukin da suka samu daga wurin gwamnati,“ in ji shi.

Kazalika, manoman sun kuma bayyana fargabarsu, kan rade-radin da ake yi na cewa; gwamnatin za ta shigo da Alkama daga ketare.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Alkama na Kasa, reshen Jihar Kano (WFAN), Alhaji Musa Shehu, ya tabbatar da jiran da manaomanta na jihar ke ci gaba da yi na samun daukin gwamnatin.

Amma ya sanar da cewa, duk da wannan jinkirin na samun daukin na gwamnatin, hakan bai hana manoman yin amfani da ‘yan kudaden da suke da shi na yin noman ranin na bana ba.

Ya kara da cewa, abin takaici ne kan gazawar gwamnatin, na cika wannan alkawari nata da ta yi musu.

“A matakin kungiyar, mun yi kokarin tattaunawa da sauran ma’aikatun da ke kula da bangaren aikin noma, domin ganin an cimma nasarar wannan shiri, wanda kuma muna da yakinin cewa; za a wanzar da shi,” a cewarsa.

Sai ya ci gaba da cewa, abin takaici, babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da ya samu wani dauki daga wurin gwamnatin.

“Muna bukatar gwamnatin ta yi mana bayani, kan rashin cika wannan alkwari nata, domin kada manoman su kara yin wata asara a nan gaba,” in ji shugaban.

Kazalika, an ruwaito cewa; duk kokarin da aka yi, domin ji daga bangaren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci ta shiyyar Jihar Kano, kan wannan batu; hakan ya ci tura.

Alkama
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Alkama
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.