ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
Alkama

Manoman rani na Alkama a Jihar Kano, na ci gaba da kokawa, kan gazawar gwamnatin tarayya, na cika alkawarinta na samar musu da dauki a karkashin shirinta na aikin noma na NAGS-AP.

A cewarsu, sun jira samun daukin daga wurin gwamnati, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da nanata alkawarin da gwamnatin ta yi.

  • Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata – Shehu Sani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Har ila yau, sun koka da cewa; gwamnatin ta sha yi musu alkawarin samar musu dauki, musamman wajen samar musu da kayan aiki a cikin rahusa, amma har zuwa yanzu, ba su gani a kas ba.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikinsu, Malam Habibu Garba da ke yin noma a Karamar Hukumar Garun Malam a jihar, ya sanar da cewa; jiran nasu ya ci gaba da kasancewa tamkar jiran gawon-shanu, na samu dauki daga wurin gwamnatin.

Gwamnatin, ta dai tsara shirin na NAGS-AP, da nufin kara bunkasa noman Alkama a cikin kasar, musamman domin a rage dogaro da shigo da ita daga ketare da kuma kara karfafa nomanta a fadin kasar baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Sai dai, abin takaici, bayan shafe watanni manoman nata na jiran daukin, amma shiru kake ji, ganin cewa; ba su samu ba har aka fara gudanar da kakar noman rani na 2026.

Rahotannin sun bayyana cewa, daukin da aka tsara za a samarwa da manoman Alkamar, ya hada da rage musu farashin kayan nomanta da samar musu da ingantaccen takin zamani, da za a iya yin amfani da su, hekta guda 3,000 da aka kiyasata.

Kazalika, an tsara cewa; kowanne manominta daya zai samu buhu mai nauyin kilo 50, na ingantaccen irin noma da buhu uku na takin zamani, kan farashin gwamnati na kashi 50.

Sai dai, wani daga cikin manoman Alkamar a jihar, Shehu Bello Bahago ya ce; shigar da manoman suka yi a cikin shirin gwamnati wasu kakar noma na baya sun amfana.

Ya yi gargadin cewa, matukar gwamnatin ta gaza cika alkawarin, hakan zai iya janyo wa manoman jihar, su gaza ci gaba da nomanta.

“Manomanta da dama, sun zuba jarinsu a kakar nomanta ta bana, musamman ganin cewa; akasarinsu sun dogara ne da daukin da suka samu daga wurin gwamnati,“ in ji shi.

Kazalika, manoman sun kuma bayyana fargabarsu, kan rade-radin da ake yi na cewa; gwamnatin za ta shigo da Alkama daga ketare.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Alkama na Kasa, reshen Jihar Kano (WFAN), Alhaji Musa Shehu, ya tabbatar da jiran da manaomanta na jihar ke ci gaba da yi na samun daukin gwamnatin.

Amma ya sanar da cewa, duk da wannan jinkirin na samun daukin na gwamnatin, hakan bai hana manoman yin amfani da ‘yan kudaden da suke da shi na yin noman ranin na bana ba.

Ya kara da cewa, abin takaici ne kan gazawar gwamnatin, na cika wannan alkawari nata da ta yi musu.

“A matakin kungiyar, mun yi kokarin tattaunawa da sauran ma’aikatun da ke kula da bangaren aikin noma, domin ganin an cimma nasarar wannan shiri, wanda kuma muna da yakinin cewa; za a wanzar da shi,” a cewarsa.

Sai ya ci gaba da cewa, abin takaici, babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da ya samu wani dauki daga wurin gwamnatin.

“Muna bukatar gwamnatin ta yi mana bayani, kan rashin cika wannan alkwari nata, domin kada manoman su kara yin wata asara a nan gaba,” in ji shugaban.

Kazalika, an ruwaito cewa; duk kokarin da aka yi, domin ji daga bangaren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci ta shiyyar Jihar Kano, kan wannan batu; hakan ya ci tura.

Alkama
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Alkama
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.