ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
Alkama

Manoman rani na Alkama a Jihar Kano, na ci gaba da kokawa, kan gazawar gwamnatin tarayya, na cika alkawarinta na samar musu da dauki a karkashin shirinta na aikin noma na NAGS-AP.

A cewarsu, sun jira samun daukin daga wurin gwamnati, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da nanata alkawarin da gwamnatin ta yi.

  • Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata – Shehu Sani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Har ila yau, sun koka da cewa; gwamnatin ta sha yi musu alkawarin samar musu dauki, musamman wajen samar musu da kayan aiki a cikin rahusa, amma har zuwa yanzu, ba su gani a kas ba.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikinsu, Malam Habibu Garba da ke yin noma a Karamar Hukumar Garun Malam a jihar, ya sanar da cewa; jiran nasu ya ci gaba da kasancewa tamkar jiran gawon-shanu, na samu dauki daga wurin gwamnatin.

Gwamnatin, ta dai tsara shirin na NAGS-AP, da nufin kara bunkasa noman Alkama a cikin kasar, musamman domin a rage dogaro da shigo da ita daga ketare da kuma kara karfafa nomanta a fadin kasar baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Sai dai, abin takaici, bayan shafe watanni manoman nata na jiran daukin, amma shiru kake ji, ganin cewa; ba su samu ba har aka fara gudanar da kakar noman rani na 2026.

Rahotannin sun bayyana cewa, daukin da aka tsara za a samarwa da manoman Alkamar, ya hada da rage musu farashin kayan nomanta da samar musu da ingantaccen takin zamani, da za a iya yin amfani da su, hekta guda 3,000 da aka kiyasata.

Kazalika, an tsara cewa; kowanne manominta daya zai samu buhu mai nauyin kilo 50, na ingantaccen irin noma da buhu uku na takin zamani, kan farashin gwamnati na kashi 50.

Sai dai, wani daga cikin manoman Alkamar a jihar, Shehu Bello Bahago ya ce; shigar da manoman suka yi a cikin shirin gwamnati wasu kakar noma na baya sun amfana.

Ya yi gargadin cewa, matukar gwamnatin ta gaza cika alkawarin, hakan zai iya janyo wa manoman jihar, su gaza ci gaba da nomanta.

“Manomanta da dama, sun zuba jarinsu a kakar nomanta ta bana, musamman ganin cewa; akasarinsu sun dogara ne da daukin da suka samu daga wurin gwamnati,“ in ji shi.

Kazalika, manoman sun kuma bayyana fargabarsu, kan rade-radin da ake yi na cewa; gwamnatin za ta shigo da Alkama daga ketare.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Alkama na Kasa, reshen Jihar Kano (WFAN), Alhaji Musa Shehu, ya tabbatar da jiran da manaomanta na jihar ke ci gaba da yi na samun daukin gwamnatin.

Amma ya sanar da cewa, duk da wannan jinkirin na samun daukin na gwamnatin, hakan bai hana manoman yin amfani da ‘yan kudaden da suke da shi na yin noman ranin na bana ba.

Ya kara da cewa, abin takaici ne kan gazawar gwamnatin, na cika wannan alkawari nata da ta yi musu.

“A matakin kungiyar, mun yi kokarin tattaunawa da sauran ma’aikatun da ke kula da bangaren aikin noma, domin ganin an cimma nasarar wannan shiri, wanda kuma muna da yakinin cewa; za a wanzar da shi,” a cewarsa.

Sai ya ci gaba da cewa, abin takaici, babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da ya samu wani dauki daga wurin gwamnatin.

“Muna bukatar gwamnatin ta yi mana bayani, kan rashin cika wannan alkwari nata, domin kada manoman su kara yin wata asara a nan gaba,” in ji shugaban.

Kazalika, an ruwaito cewa; duk kokarin da aka yi, domin ji daga bangaren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci ta shiyyar Jihar Kano, kan wannan batu; hakan ya ci tura.

Alkama
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Alkama
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.