Manoman rani na Alkama a Jihar Kano, na ci gaba da kokawa, kan gazawar gwamnatin tarayya, na cika alkawarinta na samar musu da dauki a karkashin shirinta na aikin noma na NAGS-AP.
A cewarsu, sun jira samun daukin daga wurin gwamnati, amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da nanata alkawarin da gwamnatin ta yi.
- Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata – Shehu Sani
- Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye
Har ila yau, sun koka da cewa; gwamnatin ta sha yi musu alkawarin samar musu dauki, musamman wajen samar musu da kayan aiki a cikin rahusa, amma har zuwa yanzu, ba su gani a kas ba.
Daya daga cikinsu, Malam Habibu Garba da ke yin noma a Karamar Hukumar Garun Malam a jihar, ya sanar da cewa; jiran nasu ya ci gaba da kasancewa tamkar jiran gawon-shanu, na samu dauki daga wurin gwamnatin.
Gwamnatin, ta dai tsara shirin na NAGS-AP, da nufin kara bunkasa noman Alkama a cikin kasar, musamman domin a rage dogaro da shigo da ita daga ketare da kuma kara karfafa nomanta a fadin kasar baki-daya.
Sai dai, abin takaici, bayan shafe watanni manoman nata na jiran daukin, amma shiru kake ji, ganin cewa; ba su samu ba har aka fara gudanar da kakar noman rani na 2026.
Rahotannin sun bayyana cewa, daukin da aka tsara za a samarwa da manoman Alkamar, ya hada da rage musu farashin kayan nomanta da samar musu da ingantaccen takin zamani, da za a iya yin amfani da su, hekta guda 3,000 da aka kiyasata.
Kazalika, an tsara cewa; kowanne manominta daya zai samu buhu mai nauyin kilo 50, na ingantaccen irin noma da buhu uku na takin zamani, kan farashin gwamnati na kashi 50.
Sai dai, wani daga cikin manoman Alkamar a jihar, Shehu Bello Bahago ya ce; shigar da manoman suka yi a cikin shirin gwamnati wasu kakar noma na baya sun amfana.
Ya yi gargadin cewa, matukar gwamnatin ta gaza cika alkawarin, hakan zai iya janyo wa manoman jihar, su gaza ci gaba da nomanta.
“Manomanta da dama, sun zuba jarinsu a kakar nomanta ta bana, musamman ganin cewa; akasarinsu sun dogara ne da daukin da suka samu daga wurin gwamnati,“ in ji shi.
Kazalika, manoman sun kuma bayyana fargabarsu, kan rade-radin da ake yi na cewa; gwamnatin za ta shigo da Alkama daga ketare.
Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Alkama na Kasa, reshen Jihar Kano (WFAN), Alhaji Musa Shehu, ya tabbatar da jiran da manaomanta na jihar ke ci gaba da yi na samun daukin gwamnatin.
Amma ya sanar da cewa, duk da wannan jinkirin na samun daukin na gwamnatin, hakan bai hana manoman yin amfani da ‘yan kudaden da suke da shi na yin noman ranin na bana ba.
Ya kara da cewa, abin takaici ne kan gazawar gwamnatin, na cika wannan alkawari nata da ta yi musu.
“A matakin kungiyar, mun yi kokarin tattaunawa da sauran ma’aikatun da ke kula da bangaren aikin noma, domin ganin an cimma nasarar wannan shiri, wanda kuma muna da yakinin cewa; za a wanzar da shi,” a cewarsa.
Sai ya ci gaba da cewa, abin takaici, babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da ya samu wani dauki daga wurin gwamnatin.
“Muna bukatar gwamnatin ta yi mana bayani, kan rashin cika wannan alkwari nata, domin kada manoman su kara yin wata asara a nan gaba,” in ji shugaban.
Kazalika, an ruwaito cewa; duk kokarin da aka yi, domin ji daga bangaren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci ta shiyyar Jihar Kano, kan wannan batu; hakan ya ci tura.















Discussion about this post