Tsohuwar mai bai wa Gwamna Raɗɗa shawara kan ilimin ’ya’ya mata, Hajiya Jamila Abdu Mani, ta samu nasara kan abokin takararta Ahmad Saleh Junior da gagarumin rinjaye a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC mai mulki.
Da yake bayyana sakamakon zaɓen fidda gwanin da aka gudanar a mazaɓu 22 da ke ƙananan hukumomin Bindawa da Mani, shugaban kwamitin zaɓen, Hon. Shafi’u Abdu Duwan, ya ce Hajiya Jamila Abdu Mani ta samu ƙuri’u 2,498, yayin da Ahmad Saleh Junior ya samu ƙuri’u 1,256.
Tun farko dai an yi ta ce-ce-ku-ce bayan da aka bayyana cewa an gudanar da sasanci wanda ya bai wa Jamila Abdu Mani nasara, amma abokin takararta ya ƙi amincewa da hakan, lamarin da ya kai ga gudanar da zaɓen fidda gwani.
Yanzu haka, Hajiya Jamila Abdu Mani ce mace kaɗai da ta samu tikitin takarar kujerar majalisar tarayya daga jihar Katsina a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin wakiltar ƙananan hukumomin Bindawa da Mani a zaɓen 2027.
Haka kuma, idan za a iya tunawa, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Bindawa da Mani a yanzu, Hon. Ahmad Yusuf Ibrahim na jam’iyyar APC, bai shiga wannan takara ba saboda shi ma daga ƙaramar hukumar Bindawa ya fito.
Batun tsayawarta takara ya kasance ɗaya daga cikin abubuwan da suka jawo muhawara a siyasar Jihar Katsina, musamman tsakanin malamai da masu sharhi kan al’amuran yau da kullum.
Yanzu dai abin jira a gani shi ne yadda za ta tunkari babban zaɓen, la’akari da irin ƙalubalen da ta ke fuskanta a matsayinta na mace ’yar takara daga jihar.















Discussion about this post