ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Buhari

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce yana shirin barin gidan gwamnati domin ya koma gidansa, yana aiki a gonakinsa da kiwon dabbobinsa sama da 300.

“Na kosa in bar gidan gwamnati,” in ji Buhari yake bayyana haka a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Talata yayin da yake karbar jakadiyar Amurka, Mary Beth Leonard mai barin gado.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Shema Ya Bai Wa PDP Sa’o’i 48 Ta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Masa

Ya ce idan aka yi la’akari da damar gudanar da zabe na gaskiya da kuma rashin tsoma baki kamar yadda aka gani a zabukan ranakun 25 ga Fabrairu da 18 ga Maris, ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa sun iya tantance wanda zai jagorance su ba tare da wani ya gaya musu abin da za su yi ba.

Ya nuna jin dadinsa da gagarumin kishi ga dimokuradiyya da ‘yan Nijeriya ke nunawa ta zabin da suka yi a zaben 2023.

A cewar shugaban, wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, ya ce da gaske dimokuradiyyar Nijeriya ta girma.

Ya ce: “Mutane sun fahimci ‘yancin da suke da shi. Idan aka ba da damar yin zabe na gaskiya da gaskiya, babu wanda zai iya gaya musu abin da zai yi. Ban ji dadin yadda wasu ‘yan takara suka fadi zabe ba.

“Amma na ji dadin yadda masu jefa kuri’a suka iya yanke zabar ra’ayinsu na wanda zai yi nasara da kuma wanda zai fadi. Duk da canjin kudin na rage zirga-zirgar kudade a hannun jama’a, amma sai da wasu suka raba kudin, na ce wa masu kada kuri’a su karbi kudin su yi zabi ra’ayinsu”

Ya ce ya gamsu da irin rawar da ya taka wajen gudanar da zaben ya tsaya a kansa, ba tare da tsoma baki ko wani tsangwama ba.Ya yaba wa jakadan mai barin gado cewa bisa ga dimbin nasarorin da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka cikin shekara uku da rabi. Ya bayyana fatan Nijeriya za ta ci gaba da samun ci gaba wajen gina kasa daga cikin al’ummominmu daban-daban da masu fafutuka.

Tun da farko, Leonard ta bukaci a cire tallafin mai ya daga cikin muhimman shawarwarin da Buhari zai iya dauka kafin ya bar mulki a ranar 29 ga Mayu.

Ta ce ta yi farin ciki da irin ci gaban da aka samu a dangantakar Nijeriya da Amurka a cikin shekaru uku da rabi, musamman yadda aka kafa kwanan nan na tsarin bayar da biza na tsawon shekaru biyar tsakanin kasashen biyu, aiki tare a cikin tsaro da samar da kayan aikin soji da suka hada da jiragen yaki da jirage masu saukar ungulu na yaki masu zuwa nan ba da dadewa ba, da kuma hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya don yaki da cutar kanjamau da kuma Korona tare da ba da tabbacin cewa Amurka za ta ci gaba da taimakawa wajen karfafa fannin kiwon lafiya a Nijeriya.

Ta bayyana godiyarta da na gwamnatin Amurka kan ci gaba da rawar da shugaban kasar ke takawa wajen tabbatar da tsaro a yankin Afirka da kuma karfafa tsarin dimokuradiyya a matsayin tsarin gwamnati, inda ta bayyana irin kakkausan martanin da ya bayar kan yawaitar juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka a baya-bayan nan a matsayin wanda bai dace ba.

Buhari
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.