ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

by Yusuf Shuaibu
1 month ago
Tsaro

Kungiyar manoman Nijeriya (AFAN), sashen Jihar Kaduna ta nuna damuwa kan karuwar rashin tsaro da hauhawar farashin takin zamani, wanda ta ce matsalar tsaro da tsadar kayan noma na barazana ga samar da abincii a daminar bana.

A wani hira da shugaban kungiyar na jihar, Nuhu Aminu, ya ce manoma da dama a wasu kananan hukumomi suna fuskantar kalubale wajen samun damar zuwa gonakinsu saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

Aminu ya bayyana wasu sassa na Giwa, Kauru, Kubau, Kudan, Kajuru, Sanga, da Kachia a matsayin yankunan da ke fuskantar manyan matsalolin tsaro da ke shafar ayyukan noma.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, al’ummomin karkara da yawa yanzu suna cikin tsoro yayin da ‘yan ta’adda ke ci gaba da kai hari kan kauyuka da gonaki, suna tilasta wa manoma su daina girbe amfanin gonarsu.

Rashin tsaro na shafar ayyukan noma sosai. Wasu manoma ba za su iya zuwa gonakinsu ba saboda kai hare-hare da sace-sacen mutane a yankunansu.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Aminu ya kara da cewa lamarin ya rage karfin gwiwar manoma kuma zai iya shafar samar da abinci idan ba a dauki matakan gaggawa don inganta tsaro a cikin al’ummomin da ke gudanar da harkokin manoma.

Ya kuma bayyana hauhawar farashin taki a matsayin wani babban kalubale da manoma ke fuskanta kafin lokacin shuka.

Shugaban AFAN ya ce mafi yawancin kananan noma ba za su iya siyan takin zamani ba, saboda tsadar farashi, inda ya kara da cewa kungiyar na karfafa amfani shara a matsayin taki.

A cewarsa, yayin da takin gida yake da rahusa, yawancin manoma har yanzu suna fuskantar wahala wajen sayen isassun takin da suke bukata don gudanar da harkokin nomansu.

Ya yi kira ga gwamnatoci a duk matakai su tallafa wa manoma da taki da kayan gona tun kafin lokacin noma ya kai kololuwa.

Aminu ya ce akwai bukatar gwamnati da ta bayar da karin kulawa ga aikin noma ta hanyar samar da goyon baya ga manoma, yana jaddada cewa aikin noma na ci gaba da zama daya daga cikin manyan sassan da ke daukar nauyin tattalin arzikin kasar nan.

Haka kuma, a Jihar Katsina kuwa, ta’azzarar hare-hare ya kara tada tsoro a tsakanin mazauna yankuna, da dama daga cikinsu suna cewa rashin tsaro ya ci gaba da tabarbare ayyukan noma da kasuwanci a sassan Jihar Katsina da dama.

Shugabannin al’umma sun ce hare-hare da garkuwa da mutane masu maimaitawa a kan titin Marabar Musawa zuwa Kafinsoli da sauran hanyoyin karkara sun tilasta wa manoma da dama barin gonakinsu, lamarin da ya kara tsananta rashin abinci da kuncin tattalin arziki.

Shugaban al’umma a Matazu, Malam Ibrahim Yusuf, ya ce mazauna yankin suna kara samun fargaba a lokacin da tafiya ta kama su.

“Mutanenmu suna rayuwa cikin tsoro. Manoma ba za su iya zuwa gonakinsu cikin ‘yanci ba, kuma matafiya a ko da yaushe suna cikin damuwa game da yiwuwar kai musu hari. Kowane sabon garkuwa da mutane na zurfafa damuwa da rashin tabbas a cikin al’ummominmu,” in ji shi.

Mambobin kungiyoyin al’umma a kananan hukumomin Matazu da Batsari sun bayyana al’amarin a matsayin babbar matsala da jihar ke fuskanta.

A yayin da yake zantawa da manema labarai, Musa Lawal, wani mamba a daya daga cikin kungiyoyin, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi su kara kokari wajen yakar ‘yan bindiga.

“Sace tsohon janar na soja ya nuna a fili cewa babu wanda yake da kariya. Muna bukatar a dauki mataki na gaggawa tare da karfafa bayanai sirri da kuma ci gaba da ayyukan soja don rusa wadannan kungiyoyin masu laifi,” in ji shi.

Wata mai fafutukar kare hakkin al’umma, Aisha Bello Sani, ta ce tasirin rashin tsaro a kan tattalin arzikin yankin ya zama mai tsanani.

“Yawancin kasuwanni ba sa aiki kamar yadda ya kamata, an rufe harkokin kasuwanci, kuma samar da kayan amfanin gona ya ragu saboda mutane na jin tsoron zuwa gonakinsu. Tsaro yana da alaka kai tsaye da tattalin arziki,” in ji ta.

Tsaro
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.