Kungiyar manoman Nijeriya (AFAN), sashen Jihar Kaduna ta nuna damuwa kan karuwar rashin tsaro da hauhawar farashin takin zamani, wanda ta ce matsalar tsaro da tsadar kayan noma na barazana ga samar da abincii a daminar bana.
A wani hira da shugaban kungiyar na jihar, Nuhu Aminu, ya ce manoma da dama a wasu kananan hukumomi suna fuskantar kalubale wajen samun damar zuwa gonakinsu saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.
Aminu ya bayyana wasu sassa na Giwa, Kauru, Kubau, Kudan, Kajuru, Sanga, da Kachia a matsayin yankunan da ke fuskantar manyan matsalolin tsaro da ke shafar ayyukan noma.
A cewarsa, al’ummomin karkara da yawa yanzu suna cikin tsoro yayin da ‘yan ta’adda ke ci gaba da kai hari kan kauyuka da gonaki, suna tilasta wa manoma su daina girbe amfanin gonarsu.
Rashin tsaro na shafar ayyukan noma sosai. Wasu manoma ba za su iya zuwa gonakinsu ba saboda kai hare-hare da sace-sacen mutane a yankunansu.
Aminu ya kara da cewa lamarin ya rage karfin gwiwar manoma kuma zai iya shafar samar da abinci idan ba a dauki matakan gaggawa don inganta tsaro a cikin al’ummomin da ke gudanar da harkokin manoma.
Ya kuma bayyana hauhawar farashin taki a matsayin wani babban kalubale da manoma ke fuskanta kafin lokacin shuka.
Shugaban AFAN ya ce mafi yawancin kananan noma ba za su iya siyan takin zamani ba, saboda tsadar farashi, inda ya kara da cewa kungiyar na karfafa amfani shara a matsayin taki.
A cewarsa, yayin da takin gida yake da rahusa, yawancin manoma har yanzu suna fuskantar wahala wajen sayen isassun takin da suke bukata don gudanar da harkokin nomansu.
Ya yi kira ga gwamnatoci a duk matakai su tallafa wa manoma da taki da kayan gona tun kafin lokacin noma ya kai kololuwa.
Aminu ya ce akwai bukatar gwamnati da ta bayar da karin kulawa ga aikin noma ta hanyar samar da goyon baya ga manoma, yana jaddada cewa aikin noma na ci gaba da zama daya daga cikin manyan sassan da ke daukar nauyin tattalin arzikin kasar nan.
Haka kuma, a Jihar Katsina kuwa, ta’azzarar hare-hare ya kara tada tsoro a tsakanin mazauna yankuna, da dama daga cikinsu suna cewa rashin tsaro ya ci gaba da tabarbare ayyukan noma da kasuwanci a sassan Jihar Katsina da dama.
Shugabannin al’umma sun ce hare-hare da garkuwa da mutane masu maimaitawa a kan titin Marabar Musawa zuwa Kafinsoli da sauran hanyoyin karkara sun tilasta wa manoma da dama barin gonakinsu, lamarin da ya kara tsananta rashin abinci da kuncin tattalin arziki.
Shugaban al’umma a Matazu, Malam Ibrahim Yusuf, ya ce mazauna yankin suna kara samun fargaba a lokacin da tafiya ta kama su.
“Mutanenmu suna rayuwa cikin tsoro. Manoma ba za su iya zuwa gonakinsu cikin ‘yanci ba, kuma matafiya a ko da yaushe suna cikin damuwa game da yiwuwar kai musu hari. Kowane sabon garkuwa da mutane na zurfafa damuwa da rashin tabbas a cikin al’ummominmu,” in ji shi.
Mambobin kungiyoyin al’umma a kananan hukumomin Matazu da Batsari sun bayyana al’amarin a matsayin babbar matsala da jihar ke fuskanta.
A yayin da yake zantawa da manema labarai, Musa Lawal, wani mamba a daya daga cikin kungiyoyin, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi su kara kokari wajen yakar ‘yan bindiga.
“Sace tsohon janar na soja ya nuna a fili cewa babu wanda yake da kariya. Muna bukatar a dauki mataki na gaggawa tare da karfafa bayanai sirri da kuma ci gaba da ayyukan soja don rusa wadannan kungiyoyin masu laifi,” in ji shi.
Wata mai fafutukar kare hakkin al’umma, Aisha Bello Sani, ta ce tasirin rashin tsaro a kan tattalin arzikin yankin ya zama mai tsanani.
“Yawancin kasuwanni ba sa aiki kamar yadda ya kamata, an rufe harkokin kasuwanci, kuma samar da kayan amfanin gona ya ragu saboda mutane na jin tsoron zuwa gonakinsu. Tsaro yana da alaka kai tsaye da tattalin arziki,” in ji ta.















Discussion about this post