ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mazauna Bauchi Na Kokawa Kan Tsadar Farashin Acaba Duk Da Raguwar Farashin Mai

by Khalid Idris Doya
4 months ago
bauchi

Mazauna birnin Bauchi su na ci gaba da kokawa kan tsadar farashin kuɗin sufuri na Achaba da na Keke Napep, duk da raguwar farashin kuɗin man fetur da aka samu kwanan nan.

Da dama daga cikin fasinjoji sun ce tsadar kuɗin sufuri da ke ci gaba da yin tsada ya ƙara tsananta wahalar rayuwa, musamman ga masu ƙaramin ƙarfi da ke dogaro da Achava da Keke Napep wajen zirga-zirgar yau da kullum a cikin birnin.

  • Ƴansanda Sun Cafke Wani Mahaifi Bisa Zargin Yi Wa Ƴarsa Mai Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi
  • Yadda Ɗalibai Ke Ɗaukar Darasi A Ƙasa, Cikin Rana Da Ƙarƙashin Bishiyoyi A Bauchi

A zagayen da Wakilinmu ya yi zuwa gidajen mai a ranar Talata ya tabbatar mafi yawan gidajen mai a Bauchi suna sayar da litar man fetur kan Naira N830, wanda ya ragu sosai idan aka kwatanta da tsohon farashin da ake sayar da litar mai da ya haura Naira N1,100.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan ragin, mazauna sun koka cewa kuɗin sufuri bai sauƙa ba. A cewar wasu fasinjoji, tafiyoyi da a baya ke kai N200 yanzu suna kai N400 zuwa N500, lamarin da ke ƙara janyo wahalar ga mutane.

Sun bayyana halin a matsayin rashin adalci kuma ba tare da hujja ba, suna tambayar dalilin da ya sa masu sufuri suka ƙi rage kuɗin Achava daidai da raguwar farashin mai.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Wani ma’aikacin gwamnati, Musa Abdullahi, ya ce ƙarin kuɗin sufuri ya tilasta masa rage zirga-zirgarsa tare da yin ɗan tafiya domin rage kashe kuɗin zirga-zirga.

Haka nan, wani ɗan kasuwa a Kasuwar Muda Lawal, Mustapha Mohammed, ya ce sufuri yanzu yana cin kaso mai yawa na ribar da yake samu a kullum, lamarin da ya rage masa tara riba mai tsoka.

Wani mazaunin jihar, Adamu Ashiru da ya zanta da Wakilinmu, ya ce a gaskiya wannan abun takaice ne, “Lokacin da ake sayar da litar man fetur a da baya kafin janye tallafin mai da ya sanya farashin ya tashi wurin da muke zuwa a Naira 200 ya dawo Naira 400 ko 500. To, abun takaici yanzu mai ya sauƙo daga sama da Naira 1,100 zuwa N830 amma masu abun hawa ba su sauƙo da farashin ba.”

Mazauna suna kira ga gwamnatin jihar Bauchi da ta shigo cikin lamarin ta hanyar samar da ƙarin motocin sufuri na jama’a domin sauƙaƙa matsalolin sufuri da kuma daidaita kuɗin tafiya a cikin birnin.

Wata ɗaliba a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi, Khadija Ibrahim, ta ce shigar da motocin gwamnati masu arha zai rage dogaron fasinjoji ga ‘yan Achaba masu zaman kansu tare da kawo sauƙi mai matuƙar muhimmanci.

A halin da ake ciki, wani ma’aikacin gidan mai na Matriɗ Energy Limited da ke kan titin Dass Road, Bauchi, Saleem Usman, ya shaida ana cewa farashin fetur ya sauƙa a duk faɗin jihar.

Ya ce: “Hakika farashin fetur ya sauƙa a Bauchi. Yawancin gidajen mai suna sayarwa a kan N830 kowace lita. A baya, ya haura N1,000, inda wasu ke sayarwa sama da N1,100.”

Ya ƙara da cewa gidajen mai da ke da alaƙa da Dangote, kamar MRS filling stations, suna sayar da fetur a kan N739 kowace lita.

Ƙoƙarin samun martani daga ƙungiyar masu Achaba da Keke Napep bai samu ba har zuwa lokacin kammala wannan rahoton.

bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Kai Sabon Matsayin Ci Gaba A 2025

Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Kai Sabon Matsayin Ci Gaba A 2025

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.