ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Sake Waiwayar Illolin Rabuwar Aure

by Leadership Hausa
3 years ago
Aure

Shekaru fiye da ashirin da suka gabata na taba yin wani nazari da ya ja hankalin masu karatu a jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo, wanda daga baya aka sake buga shi a wasu jaridun Hausa. A lokacin na yi rubutu ne game da illolin rabuwar aure, wanda na duba bangarori daban-daban, kama daga rayuwar iyalin da aka rabu, musamman yaran da aka haifa tare da kuma al’umma baki daya.

Abin da a karshen nazari na nuna cewa, kuskuren da wasu ma’aurata ke yi shi ne suna duba matsalar kansu ce kawai ba sa tunani kan abin da zai iya biyo baya ba, a karan kansu ko kuma ga iyalin da za su bari cikin kunci. Babu shakka, ba duk ma’auratan da ke rabuwa ne, suke yanke hukunci ido rufe ba, wasu kan dauki lokaci ana nazari da auna abubuwan da za a iya samun maslaha a kansu, har sai abin ya kure ne sannan ake hakura a yanke shawarar rabuwa gaba daya.

  • Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Neja Ya Yi Murabus Daga Kan Mukaminsa
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Fengyun-3

Wasu ma da ke rayuwar birane ko ‘yan boko, za ka ga har wajen kwararru ake zuwa, wato masana ilimin zamantakewa da sasanta tsakanin ma’aurata, don neman shawara da shiga tsakani, ana kashe makudan kudade, don dai a kaucewa rabuwa da juna a ceto aurensu da ke gab da rushewa. Don haka ba za mu zargi duk masu yanke shawarar rabuwa da juna a kan masu rashin hankali ko tunani ba. Za mu ba su uzuri kan cewa, mai yiwuwa abin da ya koro bera cikin wuta ne ya fi wutar zafi.

ADVERTISEMENT

A makon da ya gabata na samu labarin rabuwar auren da ya girgiza ni matuka, har iyali biyu, wadanda a baya na san suna zaune lafiya da juna ko kuma dai ana zaune cikin kyautatawa da hakuri da juna. Kusan dukkansu sun kasance cikin aure kimanin shekaru goma sha takwas ko kusa da haka, sun haifi yaran da suka girma suka fara mallakar hankalin kansu. Amma kwatsam, sai muka ji ai sun rabu da juna. Daya daga cikinsu wanda babu laifi idan na ambaci sunansu a nan kasancewar labarin rabuwar ya yi yawo a jaridu da sauran kafafen sadarwa, shi ne rabuwar auren Malam Al-Ameen Ciroma, dan jarida kuma jarumin finafinan Hausa a Masana’antar Kannywood, da tsohuwar matarsa Wasila Isma’il, wacce ita ma tsohuwar jarumar finafinan Hausa ce.

An ma bayyana cewa; aurensu shi ne mafi dadewa a cikin auratayyar da aka yi tsakanin jaruman masana’antar. Koda yake, kawo yanzu ba ni da masaniya kan dalilan da suka haifar da rabuwa a dukkan auren da nake magana a kai, amma har ga Allah na san su kansu da suka rabu suna cikin wani yanayi na alhini, da jujjuya abubuwan da suka faru a baya, ko suka janyo rabuwar aurensu, wanda za a iya cewa ya faru kamar a mafarki, kuma bisa kaddara. Ko kuma kamar yadda wasu ke cewa, yadda kowacce halitta ke da rai haka aure ma yana da nasa wa’adin, wanda idan ya zo karshe babu makawa sai an rabu. Za ta iya yiwuwa wani auren ya dade da rabuwa a zukatan ma’auratan, domin wasu abubuwa na auratayya a tsakaninsu tuni suka yanke, sai dai kawai ba a yanke hukunci da sanar da shaidu ba ne, sai da karshen wa’adin ya zo.

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

Wani auren kuma cike yake da zarge – zarge marasa dadi, da aibata juna ko jifan juna da sunaye iri-iri na batanci da muzantawa, alhalin a baya an nuna wa juna soyayya da kulawa. Wasu kuma dalilai ne na cin zarafi, zalunci, da tozartawa, inda za ka ji ana cewa ai da wannan zaman gara rabuwar saboda kada wani ya kashe wani, sakamakon azabtarwar da wani ke yi wa wani. Ko dai a rika nuna shi mijin ne yake dukan matarsa, da wulakanta ta, ko tauye mata hakkokinta da ke jefa rayuwarta cikin mummunan hali. Ko kuma ita matar ce take wulakanta mijin, aibata shi da cin zarafinsa, a wasu lokuta, walau da duka ko da harshenta. Tun mijin na boyewa har dai ya iya fitar da abin da ake yi masa a boye, jama’a su fahimci ukubar da yake ciki, amma ya kasa bayyanawa saboda ana ganinsa namiji, kar a gane gazawarsa.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa

Aure
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

May 1, 2026
GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

March 20, 2026
GORON JUMA’A
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

March 13, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Goyon Bayan Shimfida Zaman Lafiya A Colombia

Kasar Sin Na Goyon Bayan Shimfida Zaman Lafiya A Colombia

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.