Babban Darakta Janar na Ƙungiyar Masana’antun Nijeriya (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya bayyana cewa kusan kashi 60 cikin 100 na masana’antun da ke yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya sun daina aiki sakamakon matsalar rashin tsaro da ta daɗe tana addabar yankin.
Da yake jawabi a wani taro da Ƙungiyar Wakilan Labaran Kasuwanci da Masana’antu ta Nijeriya (CICAN) ta shirya a Legas, Ajayi-Kadir ya ɗora alhakin wannan koma baya kan ayyukan ƴan ta’adda da ƴan bindiga, waɗanda suka haddasa tangarɗa a hanyoyin samar da kayayyaki, ƙara kuɗin samarwa da kuma tilasta wa masana’antu da dama ƙaura daga yankin.
Ya bayyana cewa matsalolin tsaro sun sa kamfanoni da dama dakatar da ayyukansu, yayin da wasu wuraren masana’antu suka zama ba a amfani da su yadda ya kamata, lamarin da ya yi mummunar illa ga yanayin kasuwanci a yankin.
A cewarsa, masu zuba jari na ƙara nuna tsoron kafa sabbin masana’antu ko faɗaɗa ayyukansu a Arewa maso Gabas saboda damuwa kan tsaron jarinsu da ma’aikatansu.
“Rufe masana’antu ba wai kawai ya janyo asarar dubban ayyukan yi ba ne, har ma ya ƙara ta’azzara talauci tare da rage damar samun abin yi ga mazauna yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.
Ajayi-Kadir ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali, yana mai jaddada cewa tsaro mai inganci shi ne ginshiƙin ci gaban masana’antu mai ɗorewa.
Ya ce idan tsaro ya inganta, hakan zai ƙarfafa masana’antun da suka bar yankin su dawo, ya jawo sabbin masu zuba jari, tare da farfaɗo da harkokin tattalin arziki.
Haka kuma, ya buƙaci gwamnati ta samar da tallafi na musamman ga masana’antun da matsalar ta shafa, ciki har da inganta ababen more rayuwa, sauƙaƙa samun rance da kuma samar da wasu ƙarin ƙarfafawa domin sake gina ƙarfin masana’antu a yankin.
Ajayi-Kadir ya nuna kyakkyawan fata cewa da zarar an samu ingantaccen tsaro da ci gaba da tallafin gwamnati, yankin Arewa maso Gabas zai iya sake zama cibiyar masana’antu da kasuwanci mai muhimmanci a Nijeriya.
Ya kuma yaba wa Bola Ahmed Tinubu kan matakan da gwamnatinsa ke ɗauka wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, yana mai cewa wasu daga cikin manufofin da aka aiwatar sun fara haifar da sakamako mai kyau.
Sai dai ya lura cewa har yanzu akwai ƙalubale, musamman saboda ayyukan masu yi wa tattalin arziki zagon ƙasa, waɗanda suka hana ƴan Nijeriya da dama cin gajiyar sauye-sauyen da gwamnati ta aiwatar.
Ya jaddada muhimmancin rungumar masana’antu a matsayin wata hanya ta rage dogaro da kayayyakin ƙasashen waje da kuma ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.
Har ila yau, ya yaba wa Matatar Dangote kan muhimmiyar gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin Nijeriya, musamman wajen rage matsin lamba kan farashin man fetur a cikin gida duk da rikice-rikicen da ke faruwa a yankin Gulf.
A ƙarshe, Ajayi-Kadir ya sake jaddada ƙudirin MAN na ci gaba da kare muradun mambobinta da magance ƙalubalen da ke fuskantar bangaren masana’antu, tare da bayyana kafafen yaɗa labarai a matsayin abokan hulɗa masu muhimmanci wajen bunƙasa ƙasa.














Discussion about this post