ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 minutes ago
Tsaro

Babban Darakta Janar na Ƙungiyar Masana’antun Nijeriya (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya bayyana cewa kusan kashi 60 cikin 100 na masana’antun da ke yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya sun daina aiki sakamakon matsalar rashin tsaro da ta daɗe tana addabar yankin.

Da yake jawabi a wani taro da Ƙungiyar Wakilan Labaran Kasuwanci da Masana’antu ta Nijeriya (CICAN) ta shirya a Legas, Ajayi-Kadir ya ɗora alhakin wannan koma baya kan ayyukan ƴan ta’adda da ƴan bindiga, waɗanda suka haddasa tangarɗa a hanyoyin samar da kayayyaki, ƙara kuɗin samarwa da kuma tilasta wa masana’antu da dama ƙaura daga yankin.

Ya bayyana cewa matsalolin tsaro sun sa kamfanoni da dama dakatar da ayyukansu, yayin da wasu wuraren masana’antu suka zama ba a amfani da su yadda ya kamata, lamarin da ya yi mummunar illa ga yanayin kasuwanci a yankin.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, masu zuba jari na ƙara nuna tsoron kafa sabbin masana’antu ko faɗaɗa ayyukansu a Arewa maso Gabas saboda damuwa kan tsaron jarinsu da ma’aikatansu.

“Rufe masana’antu ba wai kawai ya janyo asarar dubban ayyukan yi ba ne, har ma ya ƙara ta’azzara talauci tare da rage damar samun abin yi ga mazauna yankunan da abin ya shafa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Ajayi-Kadir ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali, yana mai jaddada cewa tsaro mai inganci shi ne ginshiƙin ci gaban masana’antu mai ɗorewa.

Ya ce idan tsaro ya inganta, hakan zai ƙarfafa masana’antun da suka bar yankin su dawo, ya jawo sabbin masu zuba jari, tare da farfaɗo da harkokin tattalin arziki.

Haka kuma, ya buƙaci gwamnati ta samar da tallafi na musamman ga masana’antun da matsalar ta shafa, ciki har da inganta ababen more rayuwa, sauƙaƙa samun rance da kuma samar da wasu ƙarin ƙarfafawa domin sake gina ƙarfin masana’antu a yankin.

Ajayi-Kadir ya nuna kyakkyawan fata cewa da zarar an samu ingantaccen tsaro da ci gaba da tallafin gwamnati, yankin Arewa maso Gabas zai iya sake zama cibiyar masana’antu da kasuwanci mai muhimmanci a Nijeriya.

Ya kuma yaba wa Bola Ahmed Tinubu kan matakan da gwamnatinsa ke ɗauka wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, yana mai cewa wasu daga cikin manufofin da aka aiwatar sun fara haifar da sakamako mai kyau.

Sai dai ya lura cewa har yanzu akwai ƙalubale, musamman saboda ayyukan masu yi wa tattalin arziki zagon ƙasa, waɗanda suka hana ƴan Nijeriya da dama cin gajiyar sauye-sauyen da gwamnati ta aiwatar.

Ya jaddada muhimmancin rungumar masana’antu a matsayin wata hanya ta rage dogaro da kayayyakin ƙasashen waje da kuma ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Har ila yau, ya yaba wa Matatar Dangote kan muhimmiyar gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin Nijeriya, musamman wajen rage matsin lamba kan farashin man fetur a cikin gida duk da rikice-rikicen da ke faruwa a yankin Gulf.

A ƙarshe, Ajayi-Kadir ya sake jaddada ƙudirin MAN na ci gaba da kare muradun mambobinta da magance ƙalubalen da ke fuskantar bangaren masana’antu, tare da bayyana kafafen yaɗa labarai a matsayin abokan hulɗa masu muhimmanci wajen bunƙasa ƙasa.

Tsaro
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • Sulaiman
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • Sulaiman
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

MASU ALAKA

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Rahotonni

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

June 19, 2026
Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin PDP Da ADC Yau

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

June 19, 2026
Tinubu

Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

June 19, 2026
Kawayen amarya

Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina

June 19, 2026
Manzon Allah

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya

June 19, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Majalisar Wakilai Ta Fara Yunƙurin Gyaran Dokokin Soja

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Daga Ƙarshe, Tinubu Ya Naɗa Jakadu Uku Bayan Tsawon Shekara 2 Ana Jira

Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa

June 19, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.