• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
in Kasashen Ketare
0
Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Munanan hare-haren da ake kai wa dubun dubatar mazauna sansanin Zamzam ya ci gaba a kwana na uku, kamar yadda mutanen suka shaida wa BBC.

Wani mazaunin sansanin ya ce lamarin ya zama “bala’i”, wani kuma ya ce yanayin “ya ta’azzara”.

  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

An kashe sama da fararen hula 100, cikinsu har da yara akalla 20 da wata tawagar ma’aikatan lafiya a jerin hare-haren da aka fara kai wa a karshen makon da ya gabata a yankin Darfur, in ji Majalisar Dinkin Duniya (MDD).

An zargi rundunar RSF da kai hare-haren a kan birnin el-Fasher da wasu sansanoni biyu. A ranar Lahadi rundunar ta ce ta karbe iko da sansanin Zamzam amma ta musanta aikata kashe-kashen.

Sansanonin na Zamzam da Abu Shouk wata mafaka ce ga sama da mutum 700,000, da yawansu suna cikin mawuyacin hali na yunwa.

Labarai Masu Nasaba

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali

Labarin harin na zuwa ne kwana daya kafin cika shekara biyu da fara yakin basasar na Sudan tsakanin RSF da rundunar sojin kasar.

Da yake magana da BBC a safiyar Lahadi, wani mazaunin Zamzam da ke aiki da wata cibiyar da ke tallafa wa mutane da abinci ya ce an kashe “matasa da yawa”.

“An kashe masu aiki a cibiyar, haka ma an kashe likitocin da ke aikin kula da lafiya a cibiyar,” a cewar Mustafa mai shekara 34 cikin wani sakon murya ta WhatsApp.

“An kashe kawuna da dan dan’uwana. An raunata mutane kuma babu magani ko asibitin da zai kula da su – suna mutuwa saboda zubar jini.

“Har yanzu ana ci gaba kawo hari, kuma muna tunanin za a ci gaba da yin hakan har zuwa safiya.”

Ya kara da cewa an rufe dukkan hanyoyin fita daga sansanin “kuma dakaru sun zagaye duka bangarori hudu”.

Wani mutum mai suna Wasir ya ce “babu komai da ya rage a Zamzam”.

“Fararen hula masu yawa sun gudu, mu ma muna kokarin tafiya amma ba mu yi nasara ba, an rufe duka titunan, ga kuma yara a tare da mu.

Mutuwa ta ko’ina. Yanzu da nake magana da ku daga cikin wani rami, ana ta luguden wuta.”

Wasu daga cikin mazauna sansanin sun samu tserewa kuma suka yi tafiyar kilomita kamar 15 zuwa el-Fasher, a cewar Ministan Lafiya na Arewacin Darfur Ibrahim Khater.

“Na ga mutane da yawa suna barin Zamzam da kafa – akasarinsu yara, da mata, da tsofaffi,” in ji shi.

“An raunata wasu, wasu agajiye bayan an kashe ‘yan’uwansu. Lamarin ya ta’azzara.”

Jagorar tattara kayan agaji na Majalisar Dinkin Duniya a Sudan, Clementine Nkweta-Salami, ta ce “ta kadu sosai” da jin rahotonnin da ke fitowa daga Darfur.

“Wannan na nuna irin yadda ake tsananta hare-haren rashin imani kan mutanen da aka kora daga muhallansu da masu aikin agaji,” a cewarta cikin wata sanarwa.

Ita ma ma’aikatar harkokin Amurka ta yi “tir da rahotonnin hare-haren da RSF ta kai a Zamzam da kuma Abu Shouk”, tana cewa: “Muna yin Allah wadai da hare-haren RSF kan fararen hula marasa karfi.”

Kungiyar bayar da agaji ta Relief Organization ta ce ma’aikatanta tara “aka yi wa kisan rashin imani cikinsu har da likitoci, da direbobi, da wani jagoran tawaga” a harin da aka kai a Zamzam.

Kungiyar, wadda ta ce ita kadai ta rage da ke aikin kula da lafiya a sansanin, ta zargi RSF da aikata laifukan.

“Mun fahimci cewa wadannan hare-hare ne da gangan kan cibiyoyin lafiya a yankin domin hana ‘yan gudun hijira samun magani.

“Muna cikin zulumi ganin yadda aka hari daya daga cikin cibiyarmu da sauran cibiyoyin lafiya a el-Fasher.”

Kashif Shafikue, shugaban kungiyar, ya fada wa BBC cewa abin da ya faru da gangan aka aikata shi.

Kamar yadda wata ma’aikaciyar lafiya da ta tsira ta bayyana masa, ya ce mayakan RSF sun shiga wata maboyar mutane suka harbe mutum tara a ka da kuma kirjinsu.

CIkin wata sanarwa a ranar Asabar, RSF ta ce ba ita ce ta kai hare-hare kan fararen hular ba, kuma wai an shirya hare-haren ne domin a shafa mata kashin kaji.

Kwana daya bayan haka ne kuma ta ce “ta yi nasarar ‘yanta” sansanin daga hannun dakarun Sudan.

RSF ta zargi sojojin kasar da yin amfani da Zamzam “a matsayin sansanonin soji da kuma fararen hula a matsayin garkuwa”.

Wata tawagar kwararru a jami’ar Yale da ke Amurka ta ce hotunan tauraron dan’Adam da ta nazarta sun nuna “harin ya zama mafi muni da aka kai ta kasa a kan Zamzam…tun bayan fara yakin a el-Fasher cikin shekarar 2024”.

Ta ce ta lura da yadda “hare-haren amfani da wuta suka kona gine-gine da wurare da yawa a tsakiya, da kudanci, da kudu maso gabashin sansanin”.

Yakin da ake yi domin kwatar iko tsakanin RSF da sojin gwamnatin Sudan, ya jawo bala’i mafi girma a duniya a kan al’umma, inda ya tilasta wa sama da mutum miliyan 12 barin gudajensu da kuma jefa su cikin yunwa.

An fara gwabzawa a ranar 15 ga watan Afrilun 2023 bayan shugaban RSF da shugaban Sudan sun samu sabani game da makomar kasar.

El-Fasher ne gari mafi girma a yankin Darfur da ke karkashin ikon sojoji, wanda RSF suka kewaye tsawon shekara daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gudun hijiraSudan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin BRICS Ya Zama Muhimmin Dandalin Hadin Kai Na Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin

Related

Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci
Kasashen Ketare

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

2 days ago
Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali
Kasashen Ketare

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali

3 days ago
Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Kasashen Ketare

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

4 days ago
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

1 week ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

1 week ago
Next Post
Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin

Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.