ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sudan

Munanan hare-haren da ake kai wa dubun dubatar mazauna sansanin Zamzam ya ci gaba a kwana na uku, kamar yadda mutanen suka shaida wa BBC.

Wani mazaunin sansanin ya ce lamarin ya zama “bala’i”, wani kuma ya ce yanayin “ya ta’azzara”.

  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

An kashe sama da fararen hula 100, cikinsu har da yara akalla 20 da wata tawagar ma’aikatan lafiya a jerin hare-haren da aka fara kai wa a karshen makon da ya gabata a yankin Darfur, in ji Majalisar Dinkin Duniya (MDD).

ADVERTISEMENT

An zargi rundunar RSF da kai hare-haren a kan birnin el-Fasher da wasu sansanoni biyu. A ranar Lahadi rundunar ta ce ta karbe iko da sansanin Zamzam amma ta musanta aikata kashe-kashen.

Sansanonin na Zamzam da Abu Shouk wata mafaka ce ga sama da mutum 700,000, da yawansu suna cikin mawuyacin hali na yunwa.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Labarin harin na zuwa ne kwana daya kafin cika shekara biyu da fara yakin basasar na Sudan tsakanin RSF da rundunar sojin kasar.

Da yake magana da BBC a safiyar Lahadi, wani mazaunin Zamzam da ke aiki da wata cibiyar da ke tallafa wa mutane da abinci ya ce an kashe “matasa da yawa”.

“An kashe masu aiki a cibiyar, haka ma an kashe likitocin da ke aikin kula da lafiya a cibiyar,” a cewar Mustafa mai shekara 34 cikin wani sakon murya ta WhatsApp.

“An kashe kawuna da dan dan’uwana. An raunata mutane kuma babu magani ko asibitin da zai kula da su – suna mutuwa saboda zubar jini.

“Har yanzu ana ci gaba kawo hari, kuma muna tunanin za a ci gaba da yin hakan har zuwa safiya.”

Ya kara da cewa an rufe dukkan hanyoyin fita daga sansanin “kuma dakaru sun zagaye duka bangarori hudu”.

Wani mutum mai suna Wasir ya ce “babu komai da ya rage a Zamzam”.

“Fararen hula masu yawa sun gudu, mu ma muna kokarin tafiya amma ba mu yi nasara ba, an rufe duka titunan, ga kuma yara a tare da mu.

Mutuwa ta ko’ina. Yanzu da nake magana da ku daga cikin wani rami, ana ta luguden wuta.”

Wasu daga cikin mazauna sansanin sun samu tserewa kuma suka yi tafiyar kilomita kamar 15 zuwa el-Fasher, a cewar Ministan Lafiya na Arewacin Darfur Ibrahim Khater.

“Na ga mutane da yawa suna barin Zamzam da kafa – akasarinsu yara, da mata, da tsofaffi,” in ji shi.

“An raunata wasu, wasu agajiye bayan an kashe ‘yan’uwansu. Lamarin ya ta’azzara.”

Jagorar tattara kayan agaji na Majalisar Dinkin Duniya a Sudan, Clementine Nkweta-Salami, ta ce “ta kadu sosai” da jin rahotonnin da ke fitowa daga Darfur.

“Wannan na nuna irin yadda ake tsananta hare-haren rashin imani kan mutanen da aka kora daga muhallansu da masu aikin agaji,” a cewarta cikin wata sanarwa.

Ita ma ma’aikatar harkokin Amurka ta yi “tir da rahotonnin hare-haren da RSF ta kai a Zamzam da kuma Abu Shouk”, tana cewa: “Muna yin Allah wadai da hare-haren RSF kan fararen hula marasa karfi.”

Kungiyar bayar da agaji ta Relief Organization ta ce ma’aikatanta tara “aka yi wa kisan rashin imani cikinsu har da likitoci, da direbobi, da wani jagoran tawaga” a harin da aka kai a Zamzam.

Kungiyar, wadda ta ce ita kadai ta rage da ke aikin kula da lafiya a sansanin, ta zargi RSF da aikata laifukan.

“Mun fahimci cewa wadannan hare-hare ne da gangan kan cibiyoyin lafiya a yankin domin hana ‘yan gudun hijira samun magani.

“Muna cikin zulumi ganin yadda aka hari daya daga cikin cibiyarmu da sauran cibiyoyin lafiya a el-Fasher.”

Kashif Shafikue, shugaban kungiyar, ya fada wa BBC cewa abin da ya faru da gangan aka aikata shi.

Kamar yadda wata ma’aikaciyar lafiya da ta tsira ta bayyana masa, ya ce mayakan RSF sun shiga wata maboyar mutane suka harbe mutum tara a ka da kuma kirjinsu.

CIkin wata sanarwa a ranar Asabar, RSF ta ce ba ita ce ta kai hare-hare kan fararen hular ba, kuma wai an shirya hare-haren ne domin a shafa mata kashin kaji.

Kwana daya bayan haka ne kuma ta ce “ta yi nasarar ‘yanta” sansanin daga hannun dakarun Sudan.

RSF ta zargi sojojin kasar da yin amfani da Zamzam “a matsayin sansanonin soji da kuma fararen hula a matsayin garkuwa”.

Wata tawagar kwararru a jami’ar Yale da ke Amurka ta ce hotunan tauraron dan’Adam da ta nazarta sun nuna “harin ya zama mafi muni da aka kai ta kasa a kan Zamzam…tun bayan fara yakin a el-Fasher cikin shekarar 2024”.

Ta ce ta lura da yadda “hare-haren amfani da wuta suka kona gine-gine da wurare da yawa a tsakiya, da kudanci, da kudu maso gabashin sansanin”.

Yakin da ake yi domin kwatar iko tsakanin RSF da sojin gwamnatin Sudan, ya jawo bala’i mafi girma a duniya a kan al’umma, inda ya tilasta wa sama da mutum miliyan 12 barin gudajensu da kuma jefa su cikin yunwa.

An fara gwabzawa a ranar 15 ga watan Afrilun 2023 bayan shugaban RSF da shugaban Sudan sun samu sabani game da makomar kasar.

El-Fasher ne gari mafi girma a yankin Darfur da ke karkashin ikon sojoji, wanda RSF suka kewaye tsawon shekara daya.

Sudan
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin

Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.