ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Iyalina Na Zabi Buga Wa Nijeriya Kwallo A Maimakon Ingila -Ola Aina

by Abba Ibrahim Wada
2 months ago
Ola

Dan wasan bayan kungiyar kwallon kafa ta Nottingham Forest Ola Aina ya bayyana cewa dangantaka ta iyali da kuma jin cewa shi dan Nijeriya ne sun taka muhimmiyar rawa a shawarar da ya yanke na wakiltar Nijeriya maimakon Ingila a matakin kasa da kasa.

Aina, yayin da yake magana da manema labarai a Nottingham Forest, ya bayyana cewa asalinsa na Nijeriya ya jagoranci zabin da ya yi na wakiltar kasar duk da cewar zai iya wakiltar kasar Ingila, an haife shi a Southwark dake birnin Landan, amma kuma iyayensa yan Nijeriya ne, Aina ya cancanci bugawa kasashen biyu wasa inda har ya wakilci Ingila a matakin matasa na ‘yan kasa da shekara 16 da 20.

Hakazalika ya kuma samu kira daga tawagar ‘yan kasa da shekara 21 a shekarar 2015, wani mataki da ya nuna yiwuwar samun gurbi tare da babbar tawagar kasar, duk da haka a shekarar 2017 Aina ya karbi gayyatar yin atisaye tare da babbar tawagar Nijeriya (Super Eagles) a Landan.

ADVERTISEMENT

“An haife ni kuma na girma a Landan, na yanke shawarar buga wa Nijeriya wasa, shawara ce da na yanke lokacin da nake kimanin shekaru 20, daga nan ne iyayena suka bani kwarin gwiwa, damar ta zo mini kuma na yi tunanin ita ce daidai a lokacin, don haka na dauki hakan da hannu biyu”, in ji shi.

Saboda ya riga ya wakilci Ingila a matakin matasa, Aina ya bukaci amincewar FIFA domin canza kasa, amincewar ta zo a lokacin da zai fara buga wa Nijeriya wasa a wasan share fage na gasar cin kofin Duniya da suka buga da kasar Zambia a watan Oktoban shekarar 2017.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

“Iyalina suna alfahari da ni sosai, musamman lokacin da nake sanye da rigar Super Eagles, sun fi son rigar fiye da ni, saboda haka abin alfahari ne a wajena” in ji shi, tun bayan da ya sauya kasa, Aina ya fuskanci matsaloli daban-daban, inda ta kai ga an cire shi daga cikin tawagar Nijeriya a gasar cin kofin Duniya ta shekarar 2018, yayin da Super Eagles kuma ta kasa samun cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da 2026.

Duk da haka, ya samu nasara a gasar cin kofin kasashen Afirka, inda ya lashe tagulla a shekarar 2019 da azurfa a shekarar 2023, a matakin kungiya, tsohon dan wasan na Chelsea a halin yanzu yana cikin kungiyar da za ta fafata da Aston Billa a wasan kusa da na karshe na gasar UEFA Europa League.

Ola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.