Dan wasan bayan kungiyar kwallon kafa ta Nottingham Forest Ola Aina ya bayyana cewa dangantaka ta iyali da kuma jin cewa shi dan Nijeriya ne sun taka muhimmiyar rawa a shawarar da ya yanke na wakiltar Nijeriya maimakon Ingila a matakin kasa da kasa.
Aina, yayin da yake magana da manema labarai a Nottingham Forest, ya bayyana cewa asalinsa na Nijeriya ya jagoranci zabin da ya yi na wakiltar kasar duk da cewar zai iya wakiltar kasar Ingila, an haife shi a Southwark dake birnin Landan, amma kuma iyayensa yan Nijeriya ne, Aina ya cancanci bugawa kasashen biyu wasa inda har ya wakilci Ingila a matakin matasa na ‘yan kasa da shekara 16 da 20.
Hakazalika ya kuma samu kira daga tawagar ‘yan kasa da shekara 21 a shekarar 2015, wani mataki da ya nuna yiwuwar samun gurbi tare da babbar tawagar kasar, duk da haka a shekarar 2017 Aina ya karbi gayyatar yin atisaye tare da babbar tawagar Nijeriya (Super Eagles) a Landan.
“An haife ni kuma na girma a Landan, na yanke shawarar buga wa Nijeriya wasa, shawara ce da na yanke lokacin da nake kimanin shekaru 20, daga nan ne iyayena suka bani kwarin gwiwa, damar ta zo mini kuma na yi tunanin ita ce daidai a lokacin, don haka na dauki hakan da hannu biyu”, in ji shi.
Saboda ya riga ya wakilci Ingila a matakin matasa, Aina ya bukaci amincewar FIFA domin canza kasa, amincewar ta zo a lokacin da zai fara buga wa Nijeriya wasa a wasan share fage na gasar cin kofin Duniya da suka buga da kasar Zambia a watan Oktoban shekarar 2017.
“Iyalina suna alfahari da ni sosai, musamman lokacin da nake sanye da rigar Super Eagles, sun fi son rigar fiye da ni, saboda haka abin alfahari ne a wajena” in ji shi, tun bayan da ya sauya kasa, Aina ya fuskanci matsaloli daban-daban, inda ta kai ga an cire shi daga cikin tawagar Nijeriya a gasar cin kofin Duniya ta shekarar 2018, yayin da Super Eagles kuma ta kasa samun cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da 2026.
Duk da haka, ya samu nasara a gasar cin kofin kasashen Afirka, inda ya lashe tagulla a shekarar 2019 da azurfa a shekarar 2023, a matakin kungiya, tsohon dan wasan na Chelsea a halin yanzu yana cikin kungiyar da za ta fafata da Aston Billa a wasan kusa da na karshe na gasar UEFA Europa League.















Discussion about this post