ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Iyalina Na Zabi Buga Wa Nijeriya Kwallo A Maimakon Ingila -Ola Aina

by Abba Ibrahim Wada
1 month ago
Ola

Dan wasan bayan kungiyar kwallon kafa ta Nottingham Forest Ola Aina ya bayyana cewa dangantaka ta iyali da kuma jin cewa shi dan Nijeriya ne sun taka muhimmiyar rawa a shawarar da ya yanke na wakiltar Nijeriya maimakon Ingila a matakin kasa da kasa.

Aina, yayin da yake magana da manema labarai a Nottingham Forest, ya bayyana cewa asalinsa na Nijeriya ya jagoranci zabin da ya yi na wakiltar kasar duk da cewar zai iya wakiltar kasar Ingila, an haife shi a Southwark dake birnin Landan, amma kuma iyayensa yan Nijeriya ne, Aina ya cancanci bugawa kasashen biyu wasa inda har ya wakilci Ingila a matakin matasa na ‘yan kasa da shekara 16 da 20.

Hakazalika ya kuma samu kira daga tawagar ‘yan kasa da shekara 21 a shekarar 2015, wani mataki da ya nuna yiwuwar samun gurbi tare da babbar tawagar kasar, duk da haka a shekarar 2017 Aina ya karbi gayyatar yin atisaye tare da babbar tawagar Nijeriya (Super Eagles) a Landan.

ADVERTISEMENT

“An haife ni kuma na girma a Landan, na yanke shawarar buga wa Nijeriya wasa, shawara ce da na yanke lokacin da nake kimanin shekaru 20, daga nan ne iyayena suka bani kwarin gwiwa, damar ta zo mini kuma na yi tunanin ita ce daidai a lokacin, don haka na dauki hakan da hannu biyu”, in ji shi.

Saboda ya riga ya wakilci Ingila a matakin matasa, Aina ya bukaci amincewar FIFA domin canza kasa, amincewar ta zo a lokacin da zai fara buga wa Nijeriya wasa a wasan share fage na gasar cin kofin Duniya da suka buga da kasar Zambia a watan Oktoban shekarar 2017.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

“Iyalina suna alfahari da ni sosai, musamman lokacin da nake sanye da rigar Super Eagles, sun fi son rigar fiye da ni, saboda haka abin alfahari ne a wajena” in ji shi, tun bayan da ya sauya kasa, Aina ya fuskanci matsaloli daban-daban, inda ta kai ga an cire shi daga cikin tawagar Nijeriya a gasar cin kofin Duniya ta shekarar 2018, yayin da Super Eagles kuma ta kasa samun cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da 2026.

Duk da haka, ya samu nasara a gasar cin kofin kasashen Afirka, inda ya lashe tagulla a shekarar 2019 da azurfa a shekarar 2023, a matakin kungiya, tsohon dan wasan na Chelsea a halin yanzu yana cikin kungiyar da za ta fafata da Aston Billa a wasan kusa da na karshe na gasar UEFA Europa League.

Ola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.