ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda Iyalina Na Zabi Buga Wa Nijeriya Kwallo A Maimakon Ingila -Ola Aina

by Abba Ibrahim Wada
2 months ago
Ola

Dan wasan bayan kungiyar kwallon kafa ta Nottingham Forest Ola Aina ya bayyana cewa dangantaka ta iyali da kuma jin cewa shi dan Nijeriya ne sun taka muhimmiyar rawa a shawarar da ya yanke na wakiltar Nijeriya maimakon Ingila a matakin kasa da kasa.

Aina, yayin da yake magana da manema labarai a Nottingham Forest, ya bayyana cewa asalinsa na Nijeriya ya jagoranci zabin da ya yi na wakiltar kasar duk da cewar zai iya wakiltar kasar Ingila, an haife shi a Southwark dake birnin Landan, amma kuma iyayensa yan Nijeriya ne, Aina ya cancanci bugawa kasashen biyu wasa inda har ya wakilci Ingila a matakin matasa na ‘yan kasa da shekara 16 da 20.

Hakazalika ya kuma samu kira daga tawagar ‘yan kasa da shekara 21 a shekarar 2015, wani mataki da ya nuna yiwuwar samun gurbi tare da babbar tawagar kasar, duk da haka a shekarar 2017 Aina ya karbi gayyatar yin atisaye tare da babbar tawagar Nijeriya (Super Eagles) a Landan.

ADVERTISEMENT

“An haife ni kuma na girma a Landan, na yanke shawarar buga wa Nijeriya wasa, shawara ce da na yanke lokacin da nake kimanin shekaru 20, daga nan ne iyayena suka bani kwarin gwiwa, damar ta zo mini kuma na yi tunanin ita ce daidai a lokacin, don haka na dauki hakan da hannu biyu”, in ji shi.

Saboda ya riga ya wakilci Ingila a matakin matasa, Aina ya bukaci amincewar FIFA domin canza kasa, amincewar ta zo a lokacin da zai fara buga wa Nijeriya wasa a wasan share fage na gasar cin kofin Duniya da suka buga da kasar Zambia a watan Oktoban shekarar 2017.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

“Iyalina suna alfahari da ni sosai, musamman lokacin da nake sanye da rigar Super Eagles, sun fi son rigar fiye da ni, saboda haka abin alfahari ne a wajena” in ji shi, tun bayan da ya sauya kasa, Aina ya fuskanci matsaloli daban-daban, inda ta kai ga an cire shi daga cikin tawagar Nijeriya a gasar cin kofin Duniya ta shekarar 2018, yayin da Super Eagles kuma ta kasa samun cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da 2026.

Duk da haka, ya samu nasara a gasar cin kofin kasashen Afirka, inda ya lashe tagulla a shekarar 2019 da azurfa a shekarar 2023, a matakin kungiya, tsohon dan wasan na Chelsea a halin yanzu yana cikin kungiyar da za ta fafata da Aston Billa a wasan kusa da na karshe na gasar UEFA Europa League.

Ola
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.