ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Jaddada Ƙudirinta Na Kammala Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 A Kan Lokaci

by Muhammad Bashir and Sulaiman
7 months ago
NAHCON

Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya sake jaddada aniyar Hukumar na yin shiri tun da wuri, tare da ƙarfafa haɗin gwiwar hukumomi da bin ƙa’idoji da tsare-tsare, domin tabbatar da gudanar da Hajjin 2026 cikin tsari da nasara.

 

Mai taimaka wa Shugaban NAHCON kan harkokin yaɗa labarai, Ahmad Mu’azu, ya bayyana cewa Farfesa Usman ya ce Hukumar na aiki ne bisa tsarin manufofin Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, da kuma Shirin “Renewed Hope”, wanda ke bai wa walwala da jin daɗin ibadar alhazan Nijeriya muhimmanci. Ya ce NAHCON na aiki ne a ƙarƙashin kulawar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, wanda ke jaddada kammala muhimman shirye-shiryen Hajji a kan lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Lokaci Ya Yi Na Kawo Karshen Kashe-kashen Da Ake Yi A Kano
  • Yadda Ake Hada Dilka Na Amare

Shugaban Hukumar ya nuna cewa an bai wa tanadar masaukin alhazan jihohi a Makkah muhimmanci matuƙa, tare da bin ƙa’idoji da jadawalin da hukumomin Saudiyya suka gindaya.

 

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A daidai wannan lokaci, Farfesa Usman ya amince da tura tawagar manyan jami’ai zuwa Ƙasar Saudiyya nan take. Tawagar, wadda Shugaban zai jagoranta, za ta duba tare da kammala karɓar dukkan shirye-shiryen masauki da suka rage a Makkah, domin kauce wa jinkiri da tabbatar da bin dokokin Saudiyya.

 

’Yan tawagar sun haɗa da:

1. Farfesa Abubakar A. Yagawal – Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Yaɗa Bayanai da Ayyukan Laburare (PRSILS)

2. Sheikh Muhammad Bin Uthman – Mamba, Yankin Arewa maso Yamma

3. Dr. Tajudeen Oladejo – Mamba, Yankin Kudu maso Yamma

4. Hajiya Aishat Obi Ahmed – Mamba, Yankin Kudu maso Gabas

5. Dr. Mustapha Mohammed Ali – Sakatare na Hukumar

An umarci tawagar da ta kammala dukkan shirye-shiryen masauki tare da miƙa cikakken rahoto ga Hukumar nan take bayan kammala aikin.

Sai dai Shugaban Hukumar zai ci gaba da zama a Nijeriya domin tarɓar Ministan Hajji da Umrah na Ƙasar Saudiyya, Dr. Tawfiq Al-Rabiah, wanda ake sa ran zai kai ziyara Nijeriya a wannan watan, tare da ci gaba da sa ido kan ayyukan Hukumar.

Farfesa Usman ya ƙara da cewa NAHCON ta ƙarfafa tsare-tsaren cikin-gida na shugabanci, haɗin kai da sa-ido domin tabbatar da gaskiya, bin doka da ingantaccen tsarin aiwatarwa. Wannan ya haɗa da ci gaba da tuntuba da mambobin Hukumar, manyan jami’ai, masu samar da ayyuka da kuma hukumomin Saudiyya, domin bin ƙa’idojin da aka gindaya.

Ya jaddada cewa dukkan matakan Hukumar na fitowa ne bisa ikon doka da aka ba ta a matsayin hukumar da ke kula da aikin Hajji a Nijeriya. Ya ce yanke hukunci a NAHCON na tsari ne na hukuma, ana yin sa bisa ƙa’ida da haɗin kai, ba na mutum ɗaya ba, tare da kare muradun alhazan Nijeriya da ƙarfafa dangantakar Nijeriya da Ƙasar Saudiyya.

A ƙarshe, Shugaban ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki da alhazan da ke shirin tafiya cewa NAHCON na da ƙudirin gudanar da Hajjin 2026 cikin sauƙi ba tare da tangarda ba, ta hanyar ƙarfafa tsare-tsare, inganta shiri da ɗa’a, da bunƙasa ƙwarewa bisa ƙa’idojin da duniya ta amince da su. Ya kuma ce Hukumar za ta ci gaba da fitar da bayanai na hukuma ta kafafen sadarwarta yayin da shirye-shiryen Hajjin 2026 ke gudana.

NAHCON
Muhammad Bashir
+ posts Bio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
NAHCON
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Hare-haren Isra’ila Ta Sama Ya Kashe Falasɗinawa 11 A Gaza

Hare-haren Isra'ila Ta Sama Ya Kashe Falasɗinawa 11 A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.