ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasiha Ga Masu Kudin Da Ba Sa Fidda Da Zakkah Kuma Ba Sa Taimakon ‘Yan’uwa 

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Ibrahim Bala

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Barkanmu da sake kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da muke tattaunawa game da abubuwan da suke ci wa al’umma tuwo a kwaya.

A wannan gaba ina so nayi magana akan mutum biyu zuwa uku. Na farko shuwagabannin da suke sace kudin mutane, suna ganin bari su tarawa ‘ya’yansu. Na biyu masu kudin da suke tara dukiya ba sa iya yin zakkah, ba sa iya taimakon ‘yan’uwa, makota, da abokanan arziki. Na uku, ‘yan kasuwar da ba sa iya fidda zakkah, saboda kar su yi talauci, su bar ‘ya’yansu ba su samu abin da suka bari na gado ba.

ADVERTISEMENT

Ya ilahil’alamina mu sani ita dukiya da ka ke gani arziki Allah ne yake tara shi ba wai dan’adam ba. To mu ji tsoron Allah shugabanni, idan ka mutu ranar gobe alkiyama Allah zai tsaida kai, kuma za ka zo a daure da ankwa, adalcinka shi zai kwace ka. Kuma arziki da talauci na Allah ne.

A barshi ma a matsayinka na shugaba, musamman shugabanci da aka zabi mutane matsayinsu na wakilai, aka baka kudin al’umma ka cinye, ka yi musu aiki baka yii ba, ka zo ka tara to, za ka mutu. A barshi ma ka mutum baka yi talauci ba to, ka mutu ka bar dukiyar. Kuma duk tarin girman gidanka da girman gonarka, da girman ‘guest house’ dinka a dan rami dan kankani za a saka a bunne ka.

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

To, ya kamata mu sani shi arziki da talauci duk na Allah ne, in Allah ya ga dama duk arzikinka gobe sai ka wayi gari ba ka da shi. Mu ji tsoron Allah amana ce dukiya, mu yi wa mutane abin da ya kamata wanda ko bayan ka mutu ya zama sadakatul jariya, abun zai rika zuwa a kabarinka.

Ga shi dai hakkin al’umma ne aka baka aka ce ka je ka yi musu, amma in ka yi din ma ya zama sadakatul-jariya za ka rika samun lada, me makon ka wawashe kudi ka tara dukiya ka je ka batar a kasashe, ko kuma kai ta siyan guri kana ginawa. Ka manta da za ka iya mutuwa lokaci daya to, wannan shi ne.

Su kuma wadanda ba sa bayar da Zakkah ‘yan kasuwa, kasani yau in Allah ya ga dama duk abin da ka tara na arziki wallahi Allah zai iya aiko da masifa kudin nan su kare. Ka fidda zakkah ka tsira a duniya, ka fidda zakkah ka tsira a lahira.

Wannan tara dukiya da ka yi ba shi zai tsirar da kai ba, in Allah ya rike maka ita babu wanda ya isa ya tarwatsa maka dukiya. Amma bin dokoki da Allah ya tsara sai ka ga ka tsira, wanda ya baka ya ce ga yadda yake so ka yi da dan wani abu daga cikin abin da ya baka, ka ce ba za ka yi ba ai kuskure ne.

Mu sani siyan gidaje da filaye ba shi yake hana talauci ba, in Allah ya ga dama rana daya sai ya tsayar da kasuwancinka ya daukaki wani. Duk wannan ya zama izna, mun saba gani hamshakin dan kasuwa ya zo ya wayi gari babu. To, mu yi adalci in lokacin Zakkah yayi mu fitar mu taimaki mutane iya irin Zakkar da aka yarda ka yi ta a musulunci ba ta wayo, ta dabara ba, kuna bayar da dubu biyu, dubu uku, wannan rashin adalci ne.

Sannan masu kudi kuma da Allah ya hore musu kudi ta wasu hanyoyi da dama da ba sa son taimako, su ma suna gudun talauci. Sai ka ce ai kai ka yi wahalarka, a’a! idan a gida ne kai Allah ya daukaka ya baiwa arziki to, jarrabawa Allah ya baka ya ga ya za ka yi. To, ‘yan’uwa mu sani cewa arziki da talauci duka na Allah ne.

Kai dai idan Allah ya baka damar to, ka yi kokari ka yi amfani da ita ta hanyar da addinin musulunci zai alfahari ko bayan mutuwarka. A yi abubuwan da ya kamata na taimako, gashi nan. Wasu saboda talauci ma da yunwa ya kan sa su aikata ba daidai ba, amma idan aka taimaka sai a ga an dawo daidai, gashinan ana bukatar ruwa gurare da yawa, ga hanya ana bukata.

Hadisi ne ingantacce in ka yi irin wannan za ka rika samun lada ko bayan rasuwarka, ubangiji Allah ka sa mu dace ka sa mu yi kyakkyawan karshe.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Tawagar Jami’an Kiwon Lafiya Ta Sin Ta Tallafawa Marayu A Saliyo

Tawagar Jami’an Kiwon Lafiya Ta Sin Ta Tallafawa Marayu A Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.