ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kaddamar Da Shirin Sayar Wa Matatar Man Dangote Danyen Mai

by Abubakar Abba
2 years ago
NPA

Hukumar kula da tashoshin Jiragen Ruwa ta kasa NPA, ta sanar da gudunmawar da za ta bayar wajen wanzar da umarnin gwamnatin tarayya a fanin sanya ido na gudanar da aikace-aikace.

Kazalika, ta bayyana rawar da za ta taka, wajen kara tabbatar da tsaro tare da sauran masu ruwa tsaki, domin a tabbatar samun cin nasara a shirin sayar da danyen mai da sauran dangoginsa, a kan farashin Naira ga matatar mai ta Dangote.

  • GORON JUMA’A
  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100

Ta sanar da hakan ne, a cikin sanarwar da Manajin Darakta na hukumar Dakta Abubakar Dantsoho ya fitar.

ADVERTISEMENT

Dantsoho ya ce, kwamitin wanda ya kasance a karkashin kulawar hukumar, zai sanya ido wajen ganin cewa, ana sayar da danyen man a kan farashin Naira.

Manajin Daraktan ya bayyana haka ne a jawabinsa a wata ganawa da aka gudanar a jihar Legas, inda ya bayyana jin dadinsa a kan hobbasan da hukumar ke ci gaba da yi don ta sauke nayin da aka dora mata.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Dantsoho ya ci gaba da cewa, aikin ya hada da; wasu wakilai na hukumar, jami’an rundunar sojin ruwa, jami’ai daga kamfanin NNPCL da na kamfanin rukunonin Dangote.

Sauran ya ce, sun hada da; jami’an hukumar tattara haraji na kasa FIRS da na hukumar NMASA da kuma na hukumar NDLEA.

An kuma nada babbar jami’a a sashen ayyuka a hukumar NPA Madam Maureen Ogbonna, a matsayin mai kula da sashen OSS.

Kazalika, jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, karamin kwamiti na kula da sayar Danyen man a kan Naira, ya tabbatar cewa, NNPC ya tura danyen man zuwa ga matatar man Dangote, wanda aka sayar wa da kamfanin a kan Naira, a ranar daya ga watan Okutobar 2024.

Bugu da kari, a ranar 13 ga watan Satumbar 2024, kwamitin ya sanar da cewa, a zaman da majalisar zartarwa da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta, ta amince da sayar da danyen mai da sauran dangoginsa ga matatun mai na cikin gida Nijeriya, a kan farashin Naira.

Kwamitin ya sanar da cewa, daga ranar daya ga watan Okutobar 2024, NNPC ya fara tura gangunan danyen mai ga matatar mai ta Dangote da suka kai akalla 385,000 a duk rana daya, wadanda kuma za a biya kudinsu, a kan farashin Naira.

NPA
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.