ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kaddamar Da Shirin Sayar Wa Matatar Man Dangote Danyen Mai

by Abubakar Abba
2 years ago
NPA

Hukumar kula da tashoshin Jiragen Ruwa ta kasa NPA, ta sanar da gudunmawar da za ta bayar wajen wanzar da umarnin gwamnatin tarayya a fanin sanya ido na gudanar da aikace-aikace.

Kazalika, ta bayyana rawar da za ta taka, wajen kara tabbatar da tsaro tare da sauran masu ruwa tsaki, domin a tabbatar samun cin nasara a shirin sayar da danyen mai da sauran dangoginsa, a kan farashin Naira ga matatar mai ta Dangote.

  • GORON JUMA’A
  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100

Ta sanar da hakan ne, a cikin sanarwar da Manajin Darakta na hukumar Dakta Abubakar Dantsoho ya fitar.

ADVERTISEMENT

Dantsoho ya ce, kwamitin wanda ya kasance a karkashin kulawar hukumar, zai sanya ido wajen ganin cewa, ana sayar da danyen man a kan farashin Naira.

Manajin Daraktan ya bayyana haka ne a jawabinsa a wata ganawa da aka gudanar a jihar Legas, inda ya bayyana jin dadinsa a kan hobbasan da hukumar ke ci gaba da yi don ta sauke nayin da aka dora mata.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dantsoho ya ci gaba da cewa, aikin ya hada da; wasu wakilai na hukumar, jami’an rundunar sojin ruwa, jami’ai daga kamfanin NNPCL da na kamfanin rukunonin Dangote.

Sauran ya ce, sun hada da; jami’an hukumar tattara haraji na kasa FIRS da na hukumar NMASA da kuma na hukumar NDLEA.

An kuma nada babbar jami’a a sashen ayyuka a hukumar NPA Madam Maureen Ogbonna, a matsayin mai kula da sashen OSS.

Kazalika, jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, karamin kwamiti na kula da sayar Danyen man a kan Naira, ya tabbatar cewa, NNPC ya tura danyen man zuwa ga matatar man Dangote, wanda aka sayar wa da kamfanin a kan Naira, a ranar daya ga watan Okutobar 2024.

Bugu da kari, a ranar 13 ga watan Satumbar 2024, kwamitin ya sanar da cewa, a zaman da majalisar zartarwa da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta, ta amince da sayar da danyen mai da sauran dangoginsa ga matatun mai na cikin gida Nijeriya, a kan farashin Naira.

Kwamitin ya sanar da cewa, daga ranar daya ga watan Okutobar 2024, NNPC ya fara tura gangunan danyen mai ga matatar mai ta Dangote da suka kai akalla 385,000 a duk rana daya, wadanda kuma za a biya kudinsu, a kan farashin Naira.

NPA
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Next Post
MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.