Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma jigo a jam’iyyar ADC, Peter Obi, ya isa jihar Bauchi ranar Alhamis domin ganawa da Gwamna Bala Mohammed a wata muhimmiyar tattaunawa. Ganawar ta gudana ne a ɓoye a gidan gwamnatin jihar, yayin da har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanan abin da suka tattauna ba.
Sai dai ana sa ran shugabannin biyu za su yi wa manema labarai bayani bayan kammala ganawar. Ziyarar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta hasashen yiwuwar ficewar Gwamna Bala Mohammed daga PDP.
Tun a ranar 31 ga Maris, gwamnan ya nuna ADC a matsayin jam’iyyar da ya fi karkata zuwa gare ta yayin da ya karɓi tawagar shugabannin jam’iyyar karkashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal. Duk da haka, har yanzu bai bayyana karara ba.
Hakan ya biyo bayan wata ganawa da ya yi washegari da shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, tare da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, abin da ya ƙara ɗaga hankalin masu bibiyar siyasa.
A matsayinsa na shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP, ana kallon duk wani mataki da zai ɗauka a matsayin muhimmi gabanin zaɓen 2027, yayin da Obi ya ziyarci Bauchi tare da wasu manyan jagororin ADC daga Kudu maso Gabas.















Discussion about this post