ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ragargazar Sallama Da El-Rufa’i Ke Yi A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
El-Rufa’i

A makon da ya gabata ne, Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufa’i ya sha alwashin kakkabe duk wasu baragurbin ma’aikaci da ya cancanci a kore shi a gwamnatinsa da kuma rushe duk wani gini da ya cancanci rusau har zuwa ranar da zai yi bankwana da mulki.

Gwamna el-Rufa’i ya bayyana hakan ne a ranar Asabar lokacin kaddamar da littafi a kansa, wanda shahararren dan jarida, Mista Emmanuel Ado ya wallafa.

  • ‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

Gwamnan Jihar Kaduna ya kara da cewa zai ci gaba da yin rusau ne domin kawo gyara ta yadda magajinsa idan ya hau karagar mulki ba sai ya sha wahala ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Duk wani abin da muka ga bai dace ba, za mu cire shi ta yadda gwamnatin da za ta zo bayanmu, ba za ta sake yi ba. Ku sanya ido ku gani har zuwa karshen wa’adin mulkinna, za mu ci gaba da korar baragurbin ma’aikata da rushe abubuwan da ba su dace ba,” in ji Gwamna el-Rufa’i.

Gwamnan ya bayyana hakan ne kwanaki kadan bayan da gwamnatinsa ta soke izinin mallaka na wasu kadarorin tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Makarfi, inda ta sanya musu alamar rushewa.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Lokacin da el-Rufa’i ya bayyana hakan, sai wasu suka dauka hakan ba zai yiwu ba, amma wadanda suka san hali suka ce lallai zai aika. Kwatsam san aka wayi gari da yin rusau a Gbagy Billa da ke Jihar Kaduna, inda al’umma suka shiga zakulo kayansu a cikin barazugan kango. Sanan kuma gwamnatin ta rusa wasu wuraren manya na almajiran Sheikh Zakzaky a Kaduna da Zaria a tsawan kwana uku daga Asabar zuwa Litinin.

Hakazalika, Gwamnan el-Rufa’i ya amince da tsige sarakunan Piriga da Arak, Mai Martaba Jonathan Paragua Zamuna da Mai Martaba Janar Aliyu Iliyah Yammah (Mai ritaya).

Kwamishiniyar al’amuran kananan hukumomin Jihar Kaduna, Hajiya Umma Ahmad ce ta bayyana tsige sarakunan guda biyu cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin ranar Litinin, inda ta ce sarakunan biyu sun daina gudanar da ofisoshinsu daga ranar Litinin 22 ga watan Mayun 2023.

Kwamishinan ta kara da cewa matakin tsige sun ya biyo bayan shawarwarin da ma’aikatar kula da kananan hukumomi ta yi bisa tanadin sashe na 11 na dokar da ta shafi sarautu mai lamba 21 ta shekarar 2021.

A cewarta, “Hakimin Garun Kurama, Babangida Sule shi ne zai kula da al’amuran masarautar Piriga har zuwa lokacin da za a nada sabon sarki, yayin da aka umarci sakataren majalisar da ya fara aikin nadin sabon hakimin.

“Sakataren majalisar masarautar Arak shi ne zai kula da al’amuran masarautar tare da kaddamar da tsarin nada sabon sarki,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa an tunbuke rawanin Janar Iliyah Yammah ne sakamakon saba ka’ida game da batun nadin hakimai hudu sabanin wanda aka amince da shi a masarautarsa da kuma rashin zama a masarautar Arak.

Haka kuma sanarwar ta ce an tsige Sarki Jonathan Zamuna ne biyo bayan rikicin kabilanci da ya barke tsakanin al’ummar Gure da Kitimi na Piriga a karamar hukumar Lere da kuma rashin zama a cikin masarautar.

A hannu guda kuwa, kungiyar ‘yan shi’a magoya bayan Sheikh Ibrahim Zakzaky ta yi Allah wadai da matakin da gwamnatin Jihar Kadunan ta dauka na rushe wa ‘ya’yan kungiyar gine-ginansu wadanda suka hada da makarantu da asibitoci da kuma gidaje da ke a fadin Jihar Kaduna.

Shugana kungiyar ‘yan shi’a reshen Jihar Kaduna, Aliyu Umar da ake yi wa lakabi da Tirmizi, ya shaida wa BBC cewa, ba su taba tsammanin irin wannan abu zai ci gaba ba, musamman a wurare na ilimi da asibiti, inda al’umma ke haduwa na neman lafiya.

Ya ce, ‘’ Mu a matsayinmu na ‘yan’uwa musulmi almajiran malam Zakzaky, muna da hakki mu mallaki duk abin da za mu mallaka a karkashin dokokin kasar nan.

“A yanzu babban matakin da za mu dauka shi ne, addu’ar Allah ya gaggauta daukar mana fansa, na biyu kuma za mu garzaya mu je kotu kuma an riga ma an kai kara ba a fara shari’a bane.”

Ganau sun ce da tsakar dare ne wasu ma’aikatan hukumar tsara birane ta Jihar Kaduna tare da rakiyar jami’an tsaro ne suka isa makaranta da wani asibiti mallakin wasu mambobin kungiyar shi’a magoya bayan Zakzaky suka rushe.

To sai dai kuma a nata martanin, gwamnatin Jihar Kadunan ta ce an dauki matakin rushe asibiti da makarantar ne saboda wasu dalilai.
Mai Magana da yawun hukumar tsara birane ta Jihar Kadunan, Nuhu Garba dan Ayamaka, ya shaida wa BBC cewa ko da mutum ya gina gini kuma yana da izini daga hukumarsu, daga baya aka ga ya saba wa doka bisa dalilai na tsaro, to hakkin hukumar ne ta dauki matakin da ya dace.

Ya ce, “Na farko an gina wuraren ne ba tare da izini ba, sannan kuma bisa dalilai na tsaro sai da muka aike musu da takarda a kan su a daina gudanar da wasu abubuwa da ake yi a wannan wurare.”

An dai jima ana takun saka tsakanin magoya bayan Sheikh Zakzaky da kuma gwamnatin Jihar Kaduna.

Wannan lamari yana faru ne yayin da ya rage kasa da ‘yan kwanaki gwamnan Jihar Kadunan, Malam Nasiru El-Rufai ya mika mulki ga wanda zai gaje shi.

Yanzu dai jama’a na ta addu’ar samun saukin wannan lamarin tare da neman sabuwar gwamnatin Jihar Kaduna ta duba lamarin da idon basira.

El-Rufa’i
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.