• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ragargazar Sallama Da El-Rufa’i Ke Yi A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
Wata Kungiyar Siyasa Ta Yi Allah Wadai Da Rusau A Jihar Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufa’i ya sha alwashin kakkabe duk wasu baragurbin ma’aikaci da ya cancanci a kore shi a gwamnatinsa da kuma rushe duk wani gini da ya cancanci rusau har zuwa ranar da zai yi bankwana da mulki.

Gwamna el-Rufa’i ya bayyana hakan ne a ranar Asabar lokacin kaddamar da littafi a kansa, wanda shahararren dan jarida, Mista Emmanuel Ado ya wallafa.

  • ‘El-Rufa’i Ya Cancanci Yabo Wajen Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba’

Gwamnan Jihar Kaduna ya kara da cewa zai ci gaba da yin rusau ne domin kawo gyara ta yadda magajinsa idan ya hau karagar mulki ba sai ya sha wahala ba.

Ya ce, “Duk wani abin da muka ga bai dace ba, za mu cire shi ta yadda gwamnatin da za ta zo bayanmu, ba za ta sake yi ba. Ku sanya ido ku gani har zuwa karshen wa’adin mulkinna, za mu ci gaba da korar baragurbin ma’aikata da rushe abubuwan da ba su dace ba,” in ji Gwamna el-Rufa’i.

Gwamnan ya bayyana hakan ne kwanaki kadan bayan da gwamnatinsa ta soke izinin mallaka na wasu kadarorin tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Makarfi, inda ta sanya musu alamar rushewa.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Lokacin da el-Rufa’i ya bayyana hakan, sai wasu suka dauka hakan ba zai yiwu ba, amma wadanda suka san hali suka ce lallai zai aika. Kwatsam san aka wayi gari da yin rusau a Gbagy Billa da ke Jihar Kaduna, inda al’umma suka shiga zakulo kayansu a cikin barazugan kango. Sanan kuma gwamnatin ta rusa wasu wuraren manya na almajiran Sheikh Zakzaky a Kaduna da Zaria a tsawan kwana uku daga Asabar zuwa Litinin.

Hakazalika, Gwamnan el-Rufa’i ya amince da tsige sarakunan Piriga da Arak, Mai Martaba Jonathan Paragua Zamuna da Mai Martaba Janar Aliyu Iliyah Yammah (Mai ritaya).

Kwamishiniyar al’amuran kananan hukumomin Jihar Kaduna, Hajiya Umma Ahmad ce ta bayyana tsige sarakunan guda biyu cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin ranar Litinin, inda ta ce sarakunan biyu sun daina gudanar da ofisoshinsu daga ranar Litinin 22 ga watan Mayun 2023.

Kwamishinan ta kara da cewa matakin tsige sun ya biyo bayan shawarwarin da ma’aikatar kula da kananan hukumomi ta yi bisa tanadin sashe na 11 na dokar da ta shafi sarautu mai lamba 21 ta shekarar 2021.

A cewarta, “Hakimin Garun Kurama, Babangida Sule shi ne zai kula da al’amuran masarautar Piriga har zuwa lokacin da za a nada sabon sarki, yayin da aka umarci sakataren majalisar da ya fara aikin nadin sabon hakimin.

“Sakataren majalisar masarautar Arak shi ne zai kula da al’amuran masarautar tare da kaddamar da tsarin nada sabon sarki,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa an tunbuke rawanin Janar Iliyah Yammah ne sakamakon saba ka’ida game da batun nadin hakimai hudu sabanin wanda aka amince da shi a masarautarsa da kuma rashin zama a masarautar Arak.

Haka kuma sanarwar ta ce an tsige Sarki Jonathan Zamuna ne biyo bayan rikicin kabilanci da ya barke tsakanin al’ummar Gure da Kitimi na Piriga a karamar hukumar Lere da kuma rashin zama a cikin masarautar.

A hannu guda kuwa, kungiyar ‘yan shi’a magoya bayan Sheikh Ibrahim Zakzaky ta yi Allah wadai da matakin da gwamnatin Jihar Kadunan ta dauka na rushe wa ‘ya’yan kungiyar gine-ginansu wadanda suka hada da makarantu da asibitoci da kuma gidaje da ke a fadin Jihar Kaduna.

Shugana kungiyar ‘yan shi’a reshen Jihar Kaduna, Aliyu Umar da ake yi wa lakabi da Tirmizi, ya shaida wa BBC cewa, ba su taba tsammanin irin wannan abu zai ci gaba ba, musamman a wurare na ilimi da asibiti, inda al’umma ke haduwa na neman lafiya.

Ya ce, ‘’ Mu a matsayinmu na ‘yan’uwa musulmi almajiran malam Zakzaky, muna da hakki mu mallaki duk abin da za mu mallaka a karkashin dokokin kasar nan.

“A yanzu babban matakin da za mu dauka shi ne, addu’ar Allah ya gaggauta daukar mana fansa, na biyu kuma za mu garzaya mu je kotu kuma an riga ma an kai kara ba a fara shari’a bane.”

Ganau sun ce da tsakar dare ne wasu ma’aikatan hukumar tsara birane ta Jihar Kaduna tare da rakiyar jami’an tsaro ne suka isa makaranta da wani asibiti mallakin wasu mambobin kungiyar shi’a magoya bayan Zakzaky suka rushe.

To sai dai kuma a nata martanin, gwamnatin Jihar Kadunan ta ce an dauki matakin rushe asibiti da makarantar ne saboda wasu dalilai.
Mai Magana da yawun hukumar tsara birane ta Jihar Kadunan, Nuhu Garba dan Ayamaka, ya shaida wa BBC cewa ko da mutum ya gina gini kuma yana da izini daga hukumarsu, daga baya aka ga ya saba wa doka bisa dalilai na tsaro, to hakkin hukumar ne ta dauki matakin da ya dace.

Ya ce, “Na farko an gina wuraren ne ba tare da izini ba, sannan kuma bisa dalilai na tsaro sai da muka aike musu da takarda a kan su a daina gudanar da wasu abubuwa da ake yi a wannan wurare.”

An dai jima ana takun saka tsakanin magoya bayan Sheikh Zakzaky da kuma gwamnatin Jihar Kaduna.

Wannan lamari yana faru ne yayin da ya rage kasa da ‘yan kwanaki gwamnan Jihar Kadunan, Malam Nasiru El-Rufai ya mika mulki ga wanda zai gaje shi.

Yanzu dai jama’a na ta addu’ar samun saukin wannan lamarin tare da neman sabuwar gwamnatin Jihar Kaduna ta duba lamarin da idon basira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Kaddamar Da Littafin “Tambayoyi Da Amsoshi Kan Tunanin Xi Jinping Game Da Tsarin Gurguzu Mai Halayyar Musamman Ta Kasar Sin A Sabon Zamani” A Turanci

Next Post

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
El-Rufa’i
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.