ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruguntsumin Rantsar Da Sabuwar Gwamnati: Abubuwa 10 Da Suka Kamata A Sani

by Bello Hamza
3 years ago
sabuwar gwamnati

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

Tun daga farkon makon nan ne aka shiga ruguntsumin rantsar da sabon zabbaben shugaban Nijeriya Asiwaju Bola Tinubu, a matsayin shugaban tarayyar Nijeriya na 16 a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

Hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta sanar da Asiwaju Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi na shekarar 2023 in da ya lashe zaben da kuri’a 8,794,726 a takarar da ya yi a karkashin jam’iyyar APC. Bola Tinubu dai yana da shekara 70 a duniya a halin yanzu.

Ga wasu abubuwa 10 muhimmai da ya kamata al’umma su sani game da Shirin rantsar da zabbaben shugaban kasar da aka shirya yi a filin ‘Eagle Skuare’ da ke Abuja.

ADVERTISEMENT
  1.  Ana sa ran bikin zai samu halartar shugabannin kasashe 54 daga kasashen Afrika da kuma shugabanin wasu kasashen su 65 da kasashen yankin nahiyar Turai, Amurka za su halarci bikin rantsar da sabon shugaban kasar.
  2. Za a gudanar da taron ne a filin taro na ’Eagle Skuare’ da ke Abuja.
  3. Wakilan kasashe abokan Nijeriya kamar Amurka, Birtaniya, Kanada, Faransa, Saudi Arebiya, UAE, Pakistan, Chana, Jamus, Finland, Jamaica, Japan, Israila da Turkiya za su halarci taron.
  4. An shirya karramawa ga zababben shugaban kasa Bola Tinubu wanda kuma shi zai zama shugaban rundunar sojojin Nijeriya da fareti na musamman na ranar Talata 23 ga watan Mayu.
  5. A ranar 24 ga watan Mayu aka gudanar da taron majalisar zartarwa na bankwana ga ministoci a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
  6. Za a gudanar da taro na musamman na motsa jiki wanda bangaren matasa na jam’iyyar APC suka shirya ranar 25 ga watan Mayu a filin wasa na MKO Abiola da ke Abuja za kuma a yi addu’a ta musamman a masallacin kasa a ranar Juma’a 26 ga watan Mayu.
  7. Tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, zai gabatar da lacca a kan yadda za a yi amfani da dimokradiyya wajen bunkasa ci gaba al’ummar Afrika a ranar 27 ga watan Mayu.
  8. Faretin yara na ranar yara ta duniya zai gudana a ranar 27 ga watan Mayu, za kuma a yi addu’o’i na musamman a babbar cocin kasa ranar 28 ga watan Mayu.
  9. Bikin cin abinci da nuna al’adun gargajiya a babban dakin taro na fadar shugaban kasa ranar 28 ga watan Mayu.
  10. Za a yi taron cin abinci na musamman da shugabannin kasa da abokan zabbaben shugaban kasa kawai za su halarta a dakin taro na fadar shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu 2023.
sabuwar gwamnati
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Next Post
…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya

…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.