ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Barau Ya Ziyarci Sansanonin Sojoji 4, Ya Buƙaci Murƙushe Ƴan Ta’adda

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Barau

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya ziyarci sansanonin sojoji a ƙananan hukumomin Gwarzo, Shanono da Tsanyawa na Yankin Kano ta Arewa, domin ƙarfafawa gwuiwar dakarun tsaro da aka tura yankin bayan hare-haren ƴan bindiga daga jihohin makwabta. Ziyarar ta biyo bayan umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na tura sojoji, da ƴansanda da jami’an NSCDC domin daƙile barazanar tsaro a yankin.

A cewar wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ismail Mudashir, Sanata Barau ya isa Kano da misalin karfe 7 na safe, inda ya fara ziyarar ne a Lakwaya, ƙaramar hukumar Gwarzo. A nan ne ya duba jerin dakarun tsaro tare da Kwamandan Barikin Rundunar Sojin Ƙasa ta 3 Brigade, Laftanar Kanal I. Ekoh, da sauran manyan jami’an tsaro, ƙarƙashin jagorancin Kwamandan JTF na Gwarzo, Laftanar Abdullahi Sadiq.

  • Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano
  • Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

Da yake jawabi ga dakarun, Sanata Barau ya yabawa jajircewarsu wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai godewa Shugaban Ƙasa bisa gaggauta ɗaukar matakin tura su yankin. Ya buƙaci sojojin da su ci gaba da matsa lamba kan ƴan bindiga, su bi su ko’ina suke tare da korarsu daga yankunan Kano gaba ɗaya domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

ADVERTISEMENT

Daga nan, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan ya ci gaba da ziyarar sansanonin sojoji a Tsaure da Faruruwa na ƙaramar hukumar Shanono, da kuma sansanin Tsanyawa, inda ya ƙarfafa musu gwuiwa. Ya kuma buƙaci al’ummomi da su ba jami’an tsaro cikakken haɗin kai da bayanai domin tabbatar da nasarar yaƙi da ta’addanci.

A wata ganawa da shugabannin al’umma a Faruruwa, dattijo Alhaji Yahaya Bagobiri ya gode wa Sanata Barau bisa ƙoƙarinsa wajen ganin an tura jami’an tsaro da kuma aiwatar da wasu ayyukan raya ƙasa. Sanatan ya tabbatar wa jama’a cewa za a gina dam a yankin nan ba da jimawa ba, yana mai addu’ar Allah Ya kare yankin daga sake faruwar irin waɗannan hare-hare.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Barau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Hukumar Yaƙi Da Masu Safarar Mutane Ta Ceto Mutum 17 A Nasarawa

Hukumar Yaƙi Da Masu Safarar Mutane Ta Ceto Mutum 17 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.