ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Barau Ya Ziyarci Sansanonin Sojoji 4, Ya Buƙaci Murƙushe Ƴan Ta’adda

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Barau

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya ziyarci sansanonin sojoji a ƙananan hukumomin Gwarzo, Shanono da Tsanyawa na Yankin Kano ta Arewa, domin ƙarfafawa gwuiwar dakarun tsaro da aka tura yankin bayan hare-haren ƴan bindiga daga jihohin makwabta. Ziyarar ta biyo bayan umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na tura sojoji, da ƴansanda da jami’an NSCDC domin daƙile barazanar tsaro a yankin.

A cewar wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ismail Mudashir, Sanata Barau ya isa Kano da misalin karfe 7 na safe, inda ya fara ziyarar ne a Lakwaya, ƙaramar hukumar Gwarzo. A nan ne ya duba jerin dakarun tsaro tare da Kwamandan Barikin Rundunar Sojin Ƙasa ta 3 Brigade, Laftanar Kanal I. Ekoh, da sauran manyan jami’an tsaro, ƙarƙashin jagorancin Kwamandan JTF na Gwarzo, Laftanar Abdullahi Sadiq.

  • Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano
  • Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

Da yake jawabi ga dakarun, Sanata Barau ya yabawa jajircewarsu wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai godewa Shugaban Ƙasa bisa gaggauta ɗaukar matakin tura su yankin. Ya buƙaci sojojin da su ci gaba da matsa lamba kan ƴan bindiga, su bi su ko’ina suke tare da korarsu daga yankunan Kano gaba ɗaya domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

ADVERTISEMENT

Daga nan, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan ya ci gaba da ziyarar sansanonin sojoji a Tsaure da Faruruwa na ƙaramar hukumar Shanono, da kuma sansanin Tsanyawa, inda ya ƙarfafa musu gwuiwa. Ya kuma buƙaci al’ummomi da su ba jami’an tsaro cikakken haɗin kai da bayanai domin tabbatar da nasarar yaƙi da ta’addanci.

A wata ganawa da shugabannin al’umma a Faruruwa, dattijo Alhaji Yahaya Bagobiri ya gode wa Sanata Barau bisa ƙoƙarinsa wajen ganin an tura jami’an tsaro da kuma aiwatar da wasu ayyukan raya ƙasa. Sanatan ya tabbatar wa jama’a cewa za a gina dam a yankin nan ba da jimawa ba, yana mai addu’ar Allah Ya kare yankin daga sake faruwar irin waɗannan hare-hare.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Barau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
  • Abubakar Sulaiman
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Hukumar Yaƙi Da Masu Safarar Mutane Ta Ceto Mutum 17 A Nasarawa

Hukumar Yaƙi Da Masu Safarar Mutane Ta Ceto Mutum 17 A Nasarawa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.