Tsohon mai taimaka wa shugaban ƙasa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Umar Sani, ya yi iƙirarin cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya riga ya sayi fom ɗin takarar shugaban ƙasa domin zaɓen 2027.
Sani, wanda ya taɓa zama Babban Mai Taimaka wa tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, ya bayyana hakan ne a wani shiri na tashar Trust TƁ a ranar Talata.
Ya ce yana da ƙwarin gwiwa cewa shari’ar da ake ƙalubalantar cancantar Jonathan ta sake tsayawa takara kotu za ta yi watsi da ita, yana mai cewa an riga an yanke hukunci kan wannan batu a baya.
A cewarsa, kawai Kotun Ƙoli ce kaɗai za ta iya sauya hukuncin da aka yanke a baya kan cancantar Jonathan, yana mai cewa shari’ar da ke gaban Mai Shari’a Peter Lifu za a iya watsar da ita saboda rashin hurumin sauraron ta a ranar 26 ga Mayu.
Sani ya ce wannan magana na zuwa ne a daidai lokacin da Jonathan ke ci gaba da yin shawarwari a fagen siyasa, lamarin da ke ƙara jawo jita-jitar cewa yana shirin dawowa takara bayan shekaru kusan 12 da barin mulki.
Ko da yake Jonathan bai fito fili ya tabbatar da aniyarsa ba, Sani ya ce matakan da tsohon shugaban ƙasar ke ɗauka sun nuna cewa yana da burin siyasa mai ƙarfi.
Ya ce: “A siyasa, abu mafi muhimmanci shi ne aiki. Idan kana da niyya, akwai matakai da dole ka bi, ciki har da siyan fom. Ya riga ya yi hakan.”
Jonathan ya yi mulkin Nijeriya daga 2010 zuwa 2015 kafin ya sha kaye a zaɓe a hannun Muhammadu Buhari.















Discussion about this post