Sarkin Zazzau, Ahmed Nuhu Bamalli, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta bai wa sarakunan gargajiya ƙarin iko a cikin kundin tsarin mulkin ƙasa domin su iya taka rawar gani yadda ya kamata wajen tafiyar da al’amuran al’umma.
Sarkin ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wani taro, inda ya jaddada cewa sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kuma sasanta rikice-rikice a tsakanin al’umma.
Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 15
Ya ce duk da irin gudunmawar da sarakunan ke bayarwa, rashin tanadin doka da zai ba su cikakken iko yana rage tasirin ayyukansu, musamman a fannin tsaro da zaman lafiya.
A cewarsa, idan aka ba sarakunan gargajiya damar aiki a ƙarƙashin kariyar doka, hakan zai taimaka matuƙa wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar, tare da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin al’umma.
Sarkin ya kuma yi kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki su duba yiwuwar sake fasalin kundin tsarin mulki domin bai wa sarakunan gargajiya gurbi mai ƙarfi a tsarin shugabancin ƙasa.
Ya ƙara da cewa sarakunan gargajiya na kusa da al’umma fiye da kowa, don haka suna da damar fahimtar matsalolin jama’a da kuma samar da hanyoyin warware su cikin sauri da hikima.
A ƙarshe, ya jaddada cewa ƙarfafa rawar da sarakunan gargajiya ke takawa a hukumance zai taimaka wajen inganta tsaro, zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.















Discussion about this post