ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2027: Atiku, Obi Da Sauran ‘Yan Adawa Ba Za Su Tsorata Ni Ba — Tinubu

by Muhammad Bashir
2 months ago

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa babu wani ɗan adawa da zai iya tsoratar da shi gabanin zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa ya na nan daram kan tafarkin dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa.Tinubu ya faɗi hakan ne a yammacin ranar Alhamis a Abuja yayin wata ganawa da ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, inda ya yi jawabi ga magoya bayansa cikin raha da tafi.

Shugaban ya yi tsokaci kan manyan ‘yan adawa, haɗakar su a ƙarƙashin ADC da kuma babban taron jam’iyyar da aka gudanar an Abuja, yana mai sukar abin da ya kira hayaniya da rashin tsari.Ya ce, “Na saurari ra’ayoyi da dama, kuma hakan ya ƙarfafa min gwiwa. Ina shirye. Wannan wata dama ce ta kawar da talauci da jahilci, da kuma tabbatar da dimokuraɗiyya ta dore, ba hayaniya ko rashin ɗa’a irin na taron titi ba.

2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi

ADVERTISEMENT

Tikitin ADC 2027: Zan Goyi Bayan Duk Wanda Ya Yi Nasara — Atiku

”Tinubu ya ƙara da cewa dole ne a mutunta umarnin kotu, yana mai cewa, “Ba za mu amince da bijirewa umarnin kotu ba. Dole mu rungumi tsarin shari’a ko da ya yi mana daɗi ko bai yi ba.”

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Yayin da yake nuni da manyan ‘yan adawa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, Tinubu ya ce babu wanda zai iya tsoratar da shi dangane da zaɓen 2027.

“Suna so su tsorata ni? Ƙarya ce,” in ji shi, yana mai tuno yadda ya fuskanci ƙalubale a zaɓen fidda gwani da kuma babban zaɓe.

Shugaban ya ce ya saba da irin wannan gwagwarmaya a siyasarsa, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da jajircewa duk da ƙalubalen da ke gabansa.

“Na riga na bi wannan hanya, kuma ko da zan sake komawa sau da dama, zan yi hakan. Babu wata ƙasa mafi alheri kamar taka, kuma babu wanda zai gina ta sai mu da kanmu,” in ji shi.

A wani ɓangare kuma, Tinubu ya soki wasu manufofin sayar da kadarorin gwamnati da aka aiwatar a baya, yana mai yin nuni ga rawar da Atiku ya taka a lokacin da yake shugabantar Kwamitin Kula da Sayar da Kadarorin Gwamnati.

Ya ƙara da cewa zai ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ba za su yi nadama ba, yana mai cewa, “Idan ba su ga ci gaba a hanyoyi, ilimi da tattalin arziki ba, za mu ba su tabarau na Bola su gani da kyau.”A ƙarshe, shugaban ya sake jaddada cewa ba zai ja da baya ba duk da adawa, yana mai cewa: “Ba zan yi kasa a gwiwa ba.”

Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.