Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa babu wani ɗan adawa da zai iya tsoratar da shi gabanin zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa ya na nan daram kan tafarkin dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa.Tinubu ya faɗi hakan ne a yammacin ranar Alhamis a Abuja yayin wata ganawa da ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, inda ya yi jawabi ga magoya bayansa cikin raha da tafi.
Shugaban ya yi tsokaci kan manyan ‘yan adawa, haɗakar su a ƙarƙashin ADC da kuma babban taron jam’iyyar da aka gudanar an Abuja, yana mai sukar abin da ya kira hayaniya da rashin tsari.Ya ce, “Na saurari ra’ayoyi da dama, kuma hakan ya ƙarfafa min gwiwa. Ina shirye. Wannan wata dama ce ta kawar da talauci da jahilci, da kuma tabbatar da dimokuraɗiyya ta dore, ba hayaniya ko rashin ɗa’a irin na taron titi ba.
2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi
Tikitin ADC 2027: Zan Goyi Bayan Duk Wanda Ya Yi Nasara — Atiku
”Tinubu ya ƙara da cewa dole ne a mutunta umarnin kotu, yana mai cewa, “Ba za mu amince da bijirewa umarnin kotu ba. Dole mu rungumi tsarin shari’a ko da ya yi mana daɗi ko bai yi ba.”
Yayin da yake nuni da manyan ‘yan adawa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, Tinubu ya ce babu wanda zai iya tsoratar da shi dangane da zaɓen 2027.
“Suna so su tsorata ni? Ƙarya ce,” in ji shi, yana mai tuno yadda ya fuskanci ƙalubale a zaɓen fidda gwani da kuma babban zaɓe.
Shugaban ya ce ya saba da irin wannan gwagwarmaya a siyasarsa, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da jajircewa duk da ƙalubalen da ke gabansa.
“Na riga na bi wannan hanya, kuma ko da zan sake komawa sau da dama, zan yi hakan. Babu wata ƙasa mafi alheri kamar taka, kuma babu wanda zai gina ta sai mu da kanmu,” in ji shi.
A wani ɓangare kuma, Tinubu ya soki wasu manufofin sayar da kadarorin gwamnati da aka aiwatar a baya, yana mai yin nuni ga rawar da Atiku ya taka a lokacin da yake shugabantar Kwamitin Kula da Sayar da Kadarorin Gwamnati.
Ya ƙara da cewa zai ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ba za su yi nadama ba, yana mai cewa, “Idan ba su ga ci gaba a hanyoyi, ilimi da tattalin arziki ba, za mu ba su tabarau na Bola su gani da kyau.”A ƙarshe, shugaban ya sake jaddada cewa ba zai ja da baya ba duk da adawa, yana mai cewa: “Ba zan yi kasa a gwiwa ba.”















Discussion about this post