ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2027: Atiku, Obi Da Sauran ‘Yan Adawa Ba Za Su Tsorata Ni Ba — Tinubu

by Muhammad Bashir
3 months ago

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa babu wani ɗan adawa da zai iya tsoratar da shi gabanin zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa ya na nan daram kan tafarkin dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa.Tinubu ya faɗi hakan ne a yammacin ranar Alhamis a Abuja yayin wata ganawa da ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, inda ya yi jawabi ga magoya bayansa cikin raha da tafi.

Shugaban ya yi tsokaci kan manyan ‘yan adawa, haɗakar su a ƙarƙashin ADC da kuma babban taron jam’iyyar da aka gudanar an Abuja, yana mai sukar abin da ya kira hayaniya da rashin tsari.Ya ce, “Na saurari ra’ayoyi da dama, kuma hakan ya ƙarfafa min gwiwa. Ina shirye. Wannan wata dama ce ta kawar da talauci da jahilci, da kuma tabbatar da dimokuraɗiyya ta dore, ba hayaniya ko rashin ɗa’a irin na taron titi ba.

2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi

ADVERTISEMENT

Tikitin ADC 2027: Zan Goyi Bayan Duk Wanda Ya Yi Nasara — Atiku

”Tinubu ya ƙara da cewa dole ne a mutunta umarnin kotu, yana mai cewa, “Ba za mu amince da bijirewa umarnin kotu ba. Dole mu rungumi tsarin shari’a ko da ya yi mana daɗi ko bai yi ba.”

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Yayin da yake nuni da manyan ‘yan adawa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, Tinubu ya ce babu wanda zai iya tsoratar da shi dangane da zaɓen 2027.

“Suna so su tsorata ni? Ƙarya ce,” in ji shi, yana mai tuno yadda ya fuskanci ƙalubale a zaɓen fidda gwani da kuma babban zaɓe.

Shugaban ya ce ya saba da irin wannan gwagwarmaya a siyasarsa, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da jajircewa duk da ƙalubalen da ke gabansa.

“Na riga na bi wannan hanya, kuma ko da zan sake komawa sau da dama, zan yi hakan. Babu wata ƙasa mafi alheri kamar taka, kuma babu wanda zai gina ta sai mu da kanmu,” in ji shi.

A wani ɓangare kuma, Tinubu ya soki wasu manufofin sayar da kadarorin gwamnati da aka aiwatar a baya, yana mai yin nuni ga rawar da Atiku ya taka a lokacin da yake shugabantar Kwamitin Kula da Sayar da Kadarorin Gwamnati.

Ya ƙara da cewa zai ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ba za su yi nadama ba, yana mai cewa, “Idan ba su ga ci gaba a hanyoyi, ilimi da tattalin arziki ba, za mu ba su tabarau na Bola su gani da kyau.”A ƙarshe, shugaban ya sake jaddada cewa ba zai ja da baya ba duk da adawa, yana mai cewa: “Ba zan yi kasa a gwiwa ba.”

Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.