ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2027: Atiku, Obi Da Sauran ‘Yan Adawa Ba Za Su Tsorata Ni Ba — Tinubu

by Muhammad Bashir
2 months ago

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa babu wani ɗan adawa da zai iya tsoratar da shi gabanin zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa ya na nan daram kan tafarkin dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa.Tinubu ya faɗi hakan ne a yammacin ranar Alhamis a Abuja yayin wata ganawa da ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors ƙarƙashin jagorancin gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, inda ya yi jawabi ga magoya bayansa cikin raha da tafi.

Shugaban ya yi tsokaci kan manyan ‘yan adawa, haɗakar su a ƙarƙashin ADC da kuma babban taron jam’iyyar da aka gudanar an Abuja, yana mai sukar abin da ya kira hayaniya da rashin tsari.Ya ce, “Na saurari ra’ayoyi da dama, kuma hakan ya ƙarfafa min gwiwa. Ina shirye. Wannan wata dama ce ta kawar da talauci da jahilci, da kuma tabbatar da dimokuraɗiyya ta dore, ba hayaniya ko rashin ɗa’a irin na taron titi ba.

2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi

ADVERTISEMENT

Tikitin ADC 2027: Zan Goyi Bayan Duk Wanda Ya Yi Nasara — Atiku

”Tinubu ya ƙara da cewa dole ne a mutunta umarnin kotu, yana mai cewa, “Ba za mu amince da bijirewa umarnin kotu ba. Dole mu rungumi tsarin shari’a ko da ya yi mana daɗi ko bai yi ba.”

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Yayin da yake nuni da manyan ‘yan adawa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, Tinubu ya ce babu wanda zai iya tsoratar da shi dangane da zaɓen 2027.

“Suna so su tsorata ni? Ƙarya ce,” in ji shi, yana mai tuno yadda ya fuskanci ƙalubale a zaɓen fidda gwani da kuma babban zaɓe.

Shugaban ya ce ya saba da irin wannan gwagwarmaya a siyasarsa, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da jajircewa duk da ƙalubalen da ke gabansa.

“Na riga na bi wannan hanya, kuma ko da zan sake komawa sau da dama, zan yi hakan. Babu wata ƙasa mafi alheri kamar taka, kuma babu wanda zai gina ta sai mu da kanmu,” in ji shi.

A wani ɓangare kuma, Tinubu ya soki wasu manufofin sayar da kadarorin gwamnati da aka aiwatar a baya, yana mai yin nuni ga rawar da Atiku ya taka a lokacin da yake shugabantar Kwamitin Kula da Sayar da Kadarorin Gwamnati.

Ya ƙara da cewa zai ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya ba za su yi nadama ba, yana mai cewa, “Idan ba su ga ci gaba a hanyoyi, ilimi da tattalin arziki ba, za mu ba su tabarau na Bola su gani da kyau.”A ƙarshe, shugaban ya sake jaddada cewa ba zai ja da baya ba duk da adawa, yana mai cewa: “Ba zan yi kasa a gwiwa ba.”

Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.