Shugaban hukumar kula da Taahoshin Jiragen Ruwa ta kasa wato NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bai wa masu zuba jari a fannin tabbacin cewar, sauye-sauyen da hukumar ta kirkiro da su, za su kara taimaka wa, wajen kara habaka fannin.
Dakta Dantsoho, ya kuma nuna damuwarsa, duba da cewa, a yanzu Nijeriya na tarbar kaso 25 ne kacal, na Jiragen Ruwa da ke shige da fice, ta hanyoyin ruwan kasar.
Koda ya ke, shugaban ya kara da cewa, amma a Afirka ta Yamma, zirga-zirgar, ta kai sama da kaso 60
Ya yi nuni da cewa, amma wannan lamarin, tuni ya fara sauyawa, musamman duba da yadda gwamnatin tarayya ta hanyar ma’aikatar bunkasa tattalin arziki na teku, ta kirkiro da sauye-sauye ta kuma wanzar da su, musamman domin kara ciyar da fannin gaba
Dantsoho ya bayyana hakan ne, a babban taro da ma’aikatar bunkasa tattalin arziki na teku ya ahirya a babban birnin tarayyar Abuja
Ya jaddada cewa, fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar, zai ci gaba da bayar da gudunmawar sa, wajen ci ci gaba da samar da tsare-tsaren zuba jari, da za au taimaka wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar.
A cewarsa, duba da yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da samar da sauye-sauye da kuma yadda ake ci gaba samun karuwar masu zuba jari masu zaman kansu a cikin tattalin arzikin kasar, Dantsoho ya bai wa masu zuba jarin cewa, Nijeriya na da karfin da za ta iya mamaye fannin bunkasa tattalin arziki na teku, da ke a nahiyar Afirka.
Shugaban ya ci gaba da cewa, kasancewar Nijeriya mai dimbin alumma da karfin tattalin arziki, hakan ya sanya tamkar a kan gaba, fannin sufurin hada-hadar sufurin Jiragen Ruwa, musamman a Afirka ta Yamma, inda hakan ya sanya, za ta iya yin kafada da kafada da sauran kasashen duniya, kamar irinsu, kasashen Masar da Singapore. Shi kuwa a na sa jawabin ministan ma’aikatar bunkasa tattalin arziki na teku Gboyega Oyetola, ya sanar da cewa, Nijeriya na da albarkatun kasa da fadin kasa da kuma hanyoyin Jiragen Ruwa, wanda hakan, ya dora kasar a kan gaba a fannin sufurin Jiragen Ruwa.















Discussion about this post