A shekarar 2024 ce, Shugaban hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta kasa, Dakta Abubakar Dantsoho, ya shiga ofis, a matsayin shugaban NPA.
Sai dai, tun daga lokacin da ya kama aikin, akwai wasu, manyan boyayyun ayyukan ci gaba da ya samar, musamman wadanda suka kara taimaka wa, wajen kara ciyar da NPA, gaba.
Karin wani abin mahimmanci da nadinsa, a mukamin shi ne, Kasancewar sa ba dan siyasa ba, amma wanda ya jima yana bayar da gudunmawar sa, NPA tun lokacin da ya yi aikin yiwa kasa hidima a NPA a 1994, ya kuma kai matakin rike mukamai da dama, bayan an dauke shi aiki a NPA, hakan ya sanya ya kara samun damar, samar da ci gaba a hukumar.
Kafin a dada shi a mukamin, shugabancin NPA, Dantsoho, ya gaji ayyuka da dama a NPA, da suka hada da, manyan Tashoshin Jiragen Ruwan kasar wato na Apapa da kuma ta Tin Can Island, wadanda suka kasance, an kafa su shekaru da dama, da suka gabata.
Kazalika, sun kasance ba su da wani cikakken damar iya bayar da damar zirga-zirga ga manyan Jiragen Ruwa, musamman, da suka taso, daga wasu kasashe kasa da kasa da rashin samar masu da kayan aiki na zamani.
A saboda haka ne, Dantsoho ya yi amfani da zurfin iliminsa da kwarewar da ya samu a NPA a mukaman da ya rike a baya da kuma dubi da nazarin da ya yi na yawan alummar kasar nan, da yawansu, ya zarce milyan 230 tare irin karfin tattalin arzikin da ta ke da shi, a fadin nahiyar Afirka ya ga cewar, ta dace a zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwanta, zuwa daidai da matakan sauran na duniya.
Domin ya cimma wannan burin, Dantsoho ya kirkiri cikakkiyar manhajar zamantar da Tashoshin, tare da kuma samar da wasu kananan Tashoshin Jiragen Ruwan kamar dai ta Lekki da ke a jihar Legas tare da wadata su, da na’urorin zamani domin gudanar da ayyukan su.
Misali, Tashar ta Lekki ta samar da karuwar da ta kai ta kaso 20, a 2026, idan aka kwatanta da wanda aka samu, shekarar da ta wuce wanda hakan ya sanya har ta kai matakin iya samar da zirga-zirgar Jiragen Ruwa da suka kai jimlar kaso 40.
Hakazalika, ya farfado da Tashoshin Jiragen Ruwa na Warri, Koko, Sapele da Burutu da aka yi watsi da su shekaru da dama.
Dantsoho an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban kungiyar kasa da kasa ta Afirka wato AIAPH, a watan Agustan 2025. inda kuma a watanni baya, aka zabe shi a matsayin shugaba na farko, dan Nijeriya na kunzamani kula Tashoshin Jiragen Ruwa na Afirka ta Yamma wato, PMAWCA inda hakan, ya kara daga darajar sa, a yankin..
Duba da yadda ya himmatu wajen ci gaba da bunkasa fannin, ya samu sahalewar dala biliyan 1.1 daga gun gwamnatin tarayya, musamman domin samar da kayan aiki na zamani a a sabbin Tashoshin Jiragen Ruwa na Badagry, Akwa Ibom, da kuma ta Kalaba.















Discussion about this post