• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shaikh Dahiru Bauchi Bai Rasu Ba, Yana Cikin Koshin Lafiya, Cewar Ahlinsa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Shaikh Dahiru Bauchi Bai Rasu Ba, Yana Cikin Koshin Lafiya, Cewar Ahlinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadimai da makusantan fitaccen Shehin malamin darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi sun karyata jita-jitan da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa, Shehin Malamin ya rasu. 

Hadiman sun misalta labarin a matsayin kanzon kurege wanda bai da tushe balle makama kwata-kwata.

  • Zargin Zagon Kasa Kan Ciyarwa A Watan Ramadan: Gwamnan Jigawa Ya Dakatar Da Kwamishinan Kasuwanci
  • Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

Idan za a tuna dai tun a makon jiya ne aka yi ta yada labarin cewa Sheikh Dahiru Usman Bauchi na fama da jinyar rashin lafiya mai tsanani, lamarin da ma makusantansa suka karyata. Sai kuma a ‘yan kwanakin nan masu yada jita-jitan suka canza salo zuwa cewa ya ma rasu.

Da ya ke zantawa da wakilinmu Malam Daha Azhary Bauchi wanda hadimi ne na kusa ga Sheikh Dahiru, ya ce, “Maulana Shehi yana cikin koshin lafiya. Yau ma zai dawo Bauchi daga Abuja. Yau da yamma zai dawo Bauchi.”

“Wasu ne kawai ke samun wuri su shirya karya su yada domin tayar wa jama’a da hankali. Amma lallai labarin karya ne,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

Dahiru Bauchi

Kazalika, wani Hadimin babban malamin, Malam Garba shi ma ya karyata labarin da ake yadawa, “Shehi na nan da ransa. Zai dawo Bauchi a ranar Asabar saboda an rufe tafsir. Zai dawo Bauchi ne saboda a bana ba zai je Umra a kasa mai tsarki kamar yadda ya saba ba.

“Yana nan lafiya illa kawai yanayin jiki irin ta tsufa. Muna adduar Allah kara wa Shehi lafiya da nisan kwana. Su kuma masu yada jita-jitan muna addu’ar Allah shiryesu.”

Daya daga cikin ‘ya’yan Sheikh Dahiru Bauchi, Sirr Abdallah Sheikh ya wallafa shafinsa na Facebook a ranar Asabar dauke da sabbin hotunan shehin inda yake taya mahaifinsa murnar kammala tafsirin alkur’ani na bana.

Abdallah wallafa da cewa, “Alhamdulillah muna taya maulana Sheikh murnar kammala tafsirin bana 2024 lafiya, da fatan Allah ya kara lafiya ya nuna mana na shekara mai zuwa. Shehu mungode!.”

Wannan dai ba shi ne karo na farko da ake yada irin wannan jita-jitan ba, domin kuwa a lokuta mabanbanta an yada cewa Sheikh Dahiru ya rasu ya fi sau goma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Zagon Kasa Kan Ciyarwa A Watan Ramadan: Gwamnan Jigawa Ya Dakatar Da Kwamishinan Kasuwanci

Next Post

Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Related

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
Labarai

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

18 minutes ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 hour ago
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

9 hours ago
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe
Labarai

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

13 hours ago
Next Post
Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

July 10, 2025
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

July 10, 2025
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

July 9, 2025
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

July 9, 2025
An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

July 9, 2025
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

July 9, 2025
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

July 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

July 9, 2025
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

July 9, 2025
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.