• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shaikh Dahiru Bauchi Bai Rasu Ba, Yana Cikin Koshin Lafiya, Cewar Ahlinsa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Shaikh Dahiru Bauchi Bai Rasu Ba, Yana Cikin Koshin Lafiya, Cewar Ahlinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hadimai da makusantan fitaccen Shehin malamin darikar Tijjaniyya a Nijeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi sun karyata jita-jitan da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa, Shehin Malamin ya rasu. 

Hadiman sun misalta labarin a matsayin kanzon kurege wanda bai da tushe balle makama kwata-kwata.

  • Zargin Zagon Kasa Kan Ciyarwa A Watan Ramadan: Gwamnan Jigawa Ya Dakatar Da Kwamishinan Kasuwanci
  • Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

Idan za a tuna dai tun a makon jiya ne aka yi ta yada labarin cewa Sheikh Dahiru Usman Bauchi na fama da jinyar rashin lafiya mai tsanani, lamarin da ma makusantansa suka karyata. Sai kuma a ‘yan kwanakin nan masu yada jita-jitan suka canza salo zuwa cewa ya ma rasu.

Da ya ke zantawa da wakilinmu Malam Daha Azhary Bauchi wanda hadimi ne na kusa ga Sheikh Dahiru, ya ce, “Maulana Shehi yana cikin koshin lafiya. Yau ma zai dawo Bauchi daga Abuja. Yau da yamma zai dawo Bauchi.”

“Wasu ne kawai ke samun wuri su shirya karya su yada domin tayar wa jama’a da hankali. Amma lallai labarin karya ne,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Dahiru Bauchi

Kazalika, wani Hadimin babban malamin, Malam Garba shi ma ya karyata labarin da ake yadawa, “Shehi na nan da ransa. Zai dawo Bauchi a ranar Asabar saboda an rufe tafsir. Zai dawo Bauchi ne saboda a bana ba zai je Umra a kasa mai tsarki kamar yadda ya saba ba.

“Yana nan lafiya illa kawai yanayin jiki irin ta tsufa. Muna adduar Allah kara wa Shehi lafiya da nisan kwana. Su kuma masu yada jita-jitan muna addu’ar Allah shiryesu.”

Daya daga cikin ‘ya’yan Sheikh Dahiru Bauchi, Sirr Abdallah Sheikh ya wallafa shafinsa na Facebook a ranar Asabar dauke da sabbin hotunan shehin inda yake taya mahaifinsa murnar kammala tafsirin alkur’ani na bana.

Abdallah wallafa da cewa, “Alhamdulillah muna taya maulana Sheikh murnar kammala tafsirin bana 2024 lafiya, da fatan Allah ya kara lafiya ya nuna mana na shekara mai zuwa. Shehu mungode!.”

Wannan dai ba shi ne karo na farko da ake yada irin wannan jita-jitan ba, domin kuwa a lokuta mabanbanta an yada cewa Sheikh Dahiru ya rasu ya fi sau goma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Zagon Kasa Kan Ciyarwa A Watan Ramadan: Gwamnan Jigawa Ya Dakatar Da Kwamishinan Kasuwanci

Next Post

Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

Karin Kudin Hajji: Gwamna Inuwa Ya Tallafa Wa Maniyyatan Gombe Da Naira 500,000 Kowanne

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.