Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1 ga Muharram 1448AH, wadda ta zo daidai da ranar Talata, 16 ga Yuni, 2026.Yayin da Musulmi ke fara sabuwar shekarar Hijira, Shugaba Tinubu ya yi tsokaci kan muhimmancin Hijirar Annabi Muhammad (SAW) daga Makka zuwa Madina, wadda ta zama tushen kalandar Musulunci. Ya ce darussan Hijira da suka haɗa da sadaukarwa, haƙuri da kuma dogaro ga tsarin Allah, suna da muhimmanci wajen gina ƙasa mai zaman lafiya, adalci da ci gaba.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar, shugaban ya buƙaci dukkan ƴan Nijeriya, musamman Musulmi, da su yi amfani da wannan lokaci wajen sabunta jajircewarsu ga kyawawan halayen ɗan ƙasa nagari.
Ya yi kira da a rungumi ayyukan alheri, haƙuri da juna, gaskiya da kuma sadaukar da kai ga aiki, yana mai cewa waɗannan halaye suna da muhimmanci wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa, tsaro da ci gaba.
Shugaban ya kuma yi addu’ar Allah Ya sanya sabuwar shekarar Musulunci ta zo da albarka, zaman lafiya da wadata ga kowane gida, tare da ci gaba da shiryar da Nijeriya a kan tafarkin ci gaba.















Discussion about this post