ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirye-shiryen Fara Kofin Afirka: Abin Da Ya Kamata Ku Sani

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
Kofin

Kamar yadda hukumar ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka ta tsara, a ranar Lahadi 21 ga watan Disamba ne za a fara fafatawa a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka ta 2025, wadda ita ce karo na 35 da aka buga a tarihin gasar, kuma ita ce babbar gasa a Afirka.

Gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 na tattare da ƙalubale, fiye da waɗanda aka yi daga shekara 10 zuwa 15 baya, inda tawaga 24 za su kece-raini a filayen wasa tara cikin biranen ƙasar Moroko shida.

  • Kasashe Nawa Ne Suka Samu Tikitin Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?
  • Yadda Aka Haɗa Jadawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026

A baya ana buga gasar tsakanin Yuni zuwa Yuli, amma a gasar bana za a yi ne cikin watan Disamba, saboda wasannin gasar kofin duniya da za a yi a 2026 daga 15 ga watan Yuni zuwa 13 ga watan Yuli da za a gudanar a Amurka da Canada da kuma Meɗico.

ADVERTISEMENT

CAF ta tsara cewa za a yi gasar ne daga Disamban 2025 zuwa Janairun 2026. Kuma wannan shi ne a karon farko da za a yi gasar cin kofin Afirka a lokacin da ake bikin Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Sai dai akwai wasu muhimman bayanai da suka kamata a sani game da gasar, wanda ya kamata masoya ƙwallon ƙafa musamman a nahiyar Afirka su sani da kuma tarihin abubuwa da dama a gasar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Ƙasar Masar ta lashe gasar ne a shekarun 1957 da 1959 da 1986 da 1998 da 2006 da 2008 da 2010. Haka kuma ta zo a ta biyu sau uku a shekarun 19621 da 2017 da kuma 2021, sai ta zo ta uku a shekarun 1963 da 1971 da 1974, sannan ta zo ta huɗu sau uku shi ma a shekarun 1976 da 1980 da 1984.

Ƙasar da ta fi tarin nasarori, wato yawan zinare da azurfa da tagulla idan aka haɗa baki ɗaya, wato ƙasar da ta fi zuwa wasannin na ƙarshe ko kusa da ƙarshe ita ce ƙasar Nijeriya, inda jimilla ta samu nasarar lashe ko dai kofin ko ta zo ta biyu ko ta uku sau 16.

Ta lashe gasar sau uku a shekarun 1980 da 1994 da 2013, sannan ta zo ta biyu sau biyar a shekarun 1984 da 1988 da 1990 da 2000 da 2023, sai kuma ta zo ta uku sau takwas a shekarun 1976 da 1978 da 1992 da 2002 da 2004 da 2006 da 2010 da kuma shekarar 2019.

Sannan a ɓangaren wasanni da tara maki, ƙasar Masar ce kan gaba, inda ta halarci gasar sau 26, sannan a ciki ta buga wasa 111. A cikin wasannin, ta samu nasara a guda 60, ta yi canjaras sau 24, sannan aka doke ta a wasa guda 27. Idan aka yi amfani da tsarin maki, wato maki uku a nasara, da maki ɗaya a canjaras sai rashin maki a rashin nasara, ƙasar Masar tana da jimillar maki 204. Sannan ƙasar da ke biye mata ita ce Nijeriya, wacce ta je gasar sau 20,

inda ta buga wasa 104, ta samu nasara a wasa 57, ta yi canjaras a wasa guda 24, sannan aka doke ta a wasa 23, inda jimilla ta tara maki 195.

Haka kuma a ɓangaren tarihin lashe gasar a jere, ƙasar Masar ɗin ce dai ta fi samun nasara domin ƙasar ta lashe gasar sau uku a jere a shekarar 2006 da 2008 da 2010.

Ƙasashe guda uku ne suka samu nasarar lashe gasar a karon farko da suka fara zuwa gasar: Masar ta lashe gasar a shekarar 1957 da ta fara buga gasar, sai Ghana da ta lashe gasar a shekarar 1963 da ta fara buga gasar, sai kuma ƙasar Afirka ta Kudu da ta lashe gasar a shekarar 1996 da ta fara buga gasar.

A ɓangaren zura ƙwallaye a raga kuma ɗan wasan ƙasar Kamaru Samuel Eto’o ne ya fi zura ƙwallaye a tarihin gasar, inda ya zura ƙwallo 18 a wasa 29 da ya buga a gasar guda shida da ya buga.

Tsohon ɗan wasan na Barcelona da Inter Milan ya halarci gasar a shekarun 2000 da 2002 da 2004 da 2006 da 2008 da 2010. Wanda yake biye masa shi ne Laurent Pokou na ƙasar Iɓory Coast, wanda ya ci ƙwallo 14 a wasa 12 da ya buga a gasar. Sai kuma ɗan ƙwallon Nijeriya Rashidi Yekini wanda ya zura ƙwallo 13 a wasa 20.

Sannan wanda ya fara cin ƙwallo a gasar shi ne ɗan wasan ƙasar Masar, Raafat Attia, wanda ya fara zura ƙwallo a gasar ta farko. A wasan farko na gasar ta farko, wanda aka buga a ranar 10 ga watan Fabrairun shekarar 1957 wanda aka fafata tsakanin Masar da Sudan, shi ne ya zura ƙwallo ta farko a wasan wanda Masar ta samu nasara da ci 2-1.

Har ila yau, yan wasan da suka fi taka wasanni a gasar su ne Rigobert Song na ƙasar Kamaru, wanda ya wakilci ƙasar tsakanin shekarar 1998 zuwa shekarar 2010, da kuma André Ayew na ƙasar Ghana wanda ya wakilci ƙasar Ghana tsakanin shekarar 2008 zuwa shekarar 2023. Kuma kowanne daga cikinsu ya buga wasanni 36 ne a gasar.

Kofin
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Shugaban Ghana: Sin Ta Kasance Abokiyar Afirka Ta Gaske A Ko Da Yaushe

Shugaban Ghana: Sin Ta Kasance Abokiyar Afirka Ta Gaske A Ko Da Yaushe

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.