ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sirrin Kasancewar Mu Shekara Fiye Da 40 A Matsayin Mata Da Miji”

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Miji

Ya kamata aure ya kasance rayuwa na farin ciki, amma wani lokacin rashin jituwa da rigingimu na faruwa a tsakanin ma’aurata. IBRAHIM OBANSA, Lokoja da ATTAH ANTHONY, Jalingo da ACHOR ABIMAJE, Jos, sun rubuta labarin yadda wasu ma’aurata da suka kasance tare tsawon fiye da shekaru 40.

A cikin wannan zamani da aure ke faɗawa cikin ruɗani, ma’aurata dama sun samu nasarar gudanar da rayuwar aure cikin lumana fiye da shekaru 40. Ta cikin mawuyacin lokaci da saukin rayuwa da lokuta masu kyau da mara kyau, sun tsaya tare. Wasu sun samu lokutan baƙin ciki da rashin jituwa, duk da haka suna son juna tare da yin haƙuri da juriya wanda ya sa suka kasance a tare.

  • Gwamna Dauda Lawal: Tsayayyen Namiji A Siyasar Yankin Arewa Maso Yamma
  • Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida

A yayin da yake zantawa da Jaridar LEADERSHIP, wani dattijo a Jihar Kogi, Mista Emmanuel Bolagi Boro, ya danganta nasarar aurensa na shekaru 40 da haƙuri da kuma juriya. Ya jaddada cewa waɗannan halaye suna da muhimmanci ga kowace alaƙa don ta bunƙasa.

ADVERTISEMENT

Boro, wanda ya fito daga ƙauyen Ogori da ke ƙaramar hukumar Ogori-Magongo ta Jihar Kogi, ya bayyana cewa yana da dogon sanayya da matarsa, Miss Mary Yomi Aturu, wanda a yanzu ta koma Miss Mary Yomi Boro, kasancewar ya san danginta tun kafin su yi aure.

“Mun kasance mun fito daga ƙauye ɗaya. Na san ta tun da daɗewa kuma na san danginta. Duk da haka, na tattauna da ita a yayin bikin girbin shekara-shekara na cocinsu a shekarar 1975, wanda na halarta a matsayin ɗalibi na makarantar sakandare,” ya tuna.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A cewarsa, dangantakarsu ta kasance shekaru 13 kafin aure, ta hanyar ɗabi’u masu ƙarfi da kuma komawa ga Allah. “A zamaninmu, abin ƙyama ne a yi jima’i kafin aure. Akwai tsananin tsoron Allah a zuciyarmu a cikin waɗannan shekaru,” in ji shi.

Ya jaddada cewa babu wata hanyar sihiri da za a samu aure mai nasara, yana mai lura cewa fahimtar juna da jure ƙalubale suna da matukar muhimmanci.

“Abin da ya fi muhimmanci shi ne, ma’aurata su fahimci juna. Idan suka yi hakan kuma a shirye suke su jure, auren zai yi nasara. Dole ne su kuma koyi yafiya. Zai kasance akwai laifuka daga ɓangarorin biyu, amma haƙuri da yafiya zai taimaka wajen ɗorewar aure,” ya ƙara da cewa.

Mista da Misis Boro sun yi aure suna da shekaru 32 da 28, kuma Allah albarkace su da yara uku, mata biyu da namiji ɗaya, waɗanda duk sun yi aure kuma suna zaune tare da iyalansu.

“Allah ya albarkace mu da yara uku, kuma a yau dukkansu sun yi aure sun cikin farin ciki. Mu ma yanzu mun tsofa, kuma har yanzu muna godiya ga Allah,” in ji shi.

Mista Boro ya kasance tsohon darektan yaɗa labarai ne a ma’aikatar gwamnatin Jihar Kogi, yayin da matarsa ta kasance tsohuwar shugabar makarantar St Mary da ke Lakwaja.

Kazalika, wata uwargida mai shekaru 82 a Jihar Taraba, Mama Ruth Sule Pantuɓo, ta danganta tsawon rai da kwanciyar hankali na aurenta mai shekaru sama da 60 tare da Sir George Sule Pantuɓo mai shekaru 87, ikon Allah da haƙuri da fahimtar juna.

Da yake magana kan aurenta, wadda aka ɗaura tun a shekarar 1966, Mama Pantuɓo ta ce babu wani tsari na musamman na samun zaman lafiya a aure face tsoron Allah.

Ta bayyana yadda ta haɗu da mijinta, ta ce dangantakarsu ta fara ne da kasancewa abokai kafin ta koma soyayya, “kuma babu wani asiri sai dai Allah ya shiga cikin lamarin aurenmu. Allah ya kasancewa mai aminci. Muna ƙoƙarin biyayya gare shi, kuma ya taimaka mana ta hanyoyi da dama. Ya zo wurin aikina, muka zama abokai, sannan daga baya muka yi aure,” ta tuna.

Yayin da take tunani ƙalubalen aure a tsawon shekaru, tsohuwar ta ce duk da cewa kowanne aure yana da ƙalubale da farin ciki, amm fahimtar abokin zama da yadda za a warware matsala suna da muhimmanci, kamar yadda ta ce, auren na da ƙalubale, amma ya danganta da wanda ka aura da yadda kake magance matsaloli. A gare mu, mun kasance tare kuma muka ci gaba da zama tare. Ba mu taɓa rabuwa ko da na rana guda ba.”

Ta bayyana mijinta a matsayin mutum mai aiki tuƙuru kuma mai ladabi wanda ya kasance mai sadaukarwa ga aikinsa da iyalinsa, duk da cewa a wasu lokutan, yana son yi hira da abokansa. Ta ƙara da cewa sakamakon jure bambance-bambancen da ke tsakaninsu da warware matsaloli ta hanyar tattaunawa da addu’a ya taimaka musu wajen shawo kan matsalolin aurensu.

A cewarta, akwai abubuwa da yake yi da ba ta so, sannan ita ma akwai abubuwa da take yi da shi ma ba ya so, amma suna tattauna a tsakaninsu da yi addu’a, wanda shi ne silar samun nasarar aurensu.

Ta nanata cewa aure yana nufin mutane biyu masu yafiya suna zaune ƙarƙashin rufin gida guda ɗaya.

Mama Pantuɓo ta kuma jaddada muhimmancin kimar iyali, tana bayyana cewa kula da yara da kiyaye haƙƙoƙin gida ya ba da gudummawa sosai ga dangantakarsu mai ɗorewa. Ta shawarci matasan ma’aurata su yi haƙuri da juna da kuma kula da tarbiyyar ‘yaƴansu yadda ya kamata. Ta ƙara da cewa matasa ma’aurata a yau suna buƙatar haƙuri, da yawa suna samun rikici kan abubuwa marasa muhimmanci kuma ba su da haƙuri, wanda kuma da zarar kun yarda da juna dole ne ku kula da gidanku domin ku zauna tare.

Matar ta kuma yi kira ga ma’aurata su kiyaye kyakkyawar dangantaka da iyalansu, tana gargaɗin cewa rashin warware matsaloli da ƴan’uwa ta aure na iya kawo rashin daidaito a cikin aure, kuma da zarar akwai soyayya da girmamawa tsakanin miji da mata, da iyalansu, za a samu zaman lafiya.

Mama Pantuɓo ta ce bayan shekaru da yawa tare da mijinta, ta dubi baya tare da godiya ga Allah. Ta jaddada cewa duk da ƙalubalen da ba za a iya kaucewa su ba, jajircewarsu ga juna ta sa iyalinsu sun kasance cikin haɗin kai.

Wani mutum mai shekara 80 a Jihar Filato, Jacob Ajayi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa haƙuri da jimrewa da amincewa da juna su ne abubuwan da suke taimaka masa wajen samun aure mai cike da nasara.

Yayin da yake magana kan sirrin ɗorewar haɗin gwiwa a cikin aure, ya yi iƙirarin cewa samun nasarar aure ta ta’allaƙa ne wajen ɗaukar juriya ga namiji ko mace, sai dai ya nuna damuwarsa kan yayin aure a yau, inda masoya masu shirin aure ba sa gudanar da bincike kan wanda za su aura kafin su shiga daga ciki.

“Suna karkatar da hankalinsu ga abubuwa na wucin gadi kamar kyau da ilimi da mahaifinta, ko mahaifinsa mai dukiya. Waɗannan ba za su tabbatar da samun aure mai nasara ba,” ya bayyana.

Ya ba da shawarar ga ma’aurata masu niyya yin aure a ko da yaushe su binciki abokin da za su aura, kamar danginsa kafin su shiga aure. Ya ƙara da cewa ya kasance ka san komi gami da shi ko game da ita.

Pa Ajayi ya kuma bayyana cewa akwai lokacin da shekaru ko kyawu za su shuɗe, amma hali zai ci gaba da kasancewa cikakke.

“Ba za ka iya sa ran samun aure mai nasara ba idan ka fito daga dangin da ake sakin aure da masu shan giya da mutane masu zinace-zinace, wanda matansu ba su zama wuri guda ba,” in ji shi.

Ya shawarci ma’aurata su kasance masu haƙuri da girmama juna da kuma jin tsoron Allah, domin wannan yana cikin littafi Mai Tsarki, kuma ka da su bari abubuwa marasa ɗorewa su ja hankalinsu, kamar motoci masu kyau da gidaje masu kyau da dukiyar ban mamaki. “Me zai faru idan kyau ya shuɗe, ba motoci, ba gidaje da kuma dukiya sun tafi? Za ku rabu ne?” ya tambaya.

Ajayi ya ce ya yi aure a shekarar 1970 kuma zuwa watan Yuni, aurensa zai cika shekaru 56.

“Na haɗu da matata ta hanyar wani abokina lokacin da take zaune tare da babban yayanta, wanda ya kasance ma’aikacin tsohuwar hukumar kasuwancin jihohin Arewa (NSMB),” ya tuna.

A cewarsa, kafin wannan lokaci, yana soyayya da mata da yawa, wasu daga cikinsu malamai ne, wasu kuma ma’aikatan jinya ne, amma ya ɗauki lokaci kafin ya je ya auri matarsa, Esther, saboda ba ta cikin irin mutanen da suka yi fice, wato tana daga cikin mutane masu kamun kai kuma ba ta rayuwar ƙarya da yawancin mata ke yi a wannan zamani.

 

Miji
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Tsarin Siyasar Kano: Ya Kamata Gwamna Abba Ya Yunkura…

APC Ta Gabatar Da Mutane Uku Domin Cike Muƙamin Kujerar Mataimakin Gwamnan Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.