ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ƙwato Dabbobi 257 Da Aka Sace A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Sojoji

Sojojin Rundunar Haɗin Gwiwa a Gwarzo, ƙarƙashin jagorancin jami’an 3 Brigade, Nigerian Army na Sojojin Nijeriya, sun daƙile wani yunƙurin satar shanu a Jihar Kano, inda suka ceto dabbobi 257.

Wannan aikin ya biyo bayan kiran gaggawa da aka samu da safiyar Lahadi, kimanin ƙarfe 6:57 na safe, inda aka bayar da rahoton cewa ’yan fashi sun sace shanu daga ƙauyen Mainika a Ƙaramar Hukumar Gwarzo.

  • Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Biyayyar Siyasa A Rundunar Sojoji Domin Bunkasa Zamanantar Da Tsaron Kasa
  • Kiwon Awakan Alfarma Na Ƙara Haɓaka A Jihar Kano

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin, Mataimakin Darakta na Hulɗa da Jama’a na Sojojin Ƙasa, 3 Brigade, Major Babatunde Zubairu, ya ce sojojin sun tashi cikin sauri zuwa wata hanyar da ake zargin ’yan fashi suna bi, inda suka tare ’yan fashin da ke gudu a ƙauyen Dayi.

ADVERTISEMENT

“Da safiyar 1 ga Maris, 2026, kimanin ƙarfe 0657 na safe, sojojin JTF, a martani ga kiran gaggawa, sun tashi cikin sauri zuwa wata hanyar da ake zargin ’yan fashi suna bi, suka yi nasarar tare da yaƙi da wani rukuni na ’yan fashi masu makami a ƙauyen Dayi, waɗanda suka sace shanu daga ƙauyen Mainika a baya.

“Da suka haɗu da sojojin Rundunar Haɗin Gwiwa, ’yan fashin sun gudu cikin hargitsi zuwa Ƙaramar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina, suka bar dabbobin da suka sace, waɗanda sojojin suka ceto cikin nasara,” kamar yadda wani ɓangare na sanarwar ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Dabbobin da aka ceto sun haɗa da shanu 135, tumaki 119, akuya 1 da jakuna 2, jimillar dabbobi 257.

“An miƙa dabbobin da aka ceto, wanda ya haɗa da shanu 135, tumaki 119, akuya 1 da jakuna 2, jimillar dabbobi 257, ga masu su ta hanyar hukumomin ƙasa,” a cewar sanarwar.

Sojojin sun ce ’yan fashin sun sami mummunar asara yayin yaƙin.

“’Yan fashin sun yi mummunan asara yayin yaƙin,” in ji sanarwar.

Rundunar Haɗin Gwiwa a Gwarzo ta haɗa sojojin 3 Brigade na Sojojin Nijeriya, ‘Nigeria Police Force, Department of State Serɓices’, Nigeria Security and Ciɓil Defence Corps’, da masu sa ido na ƙasa.

Kwamandan 3 Brigade, Soja Janar Ahmad Tukur, ya yaba da jarumtaka, ƙarfin hali da ƙwarewar sojojin, inda ya ce ƙwarin gwiwa da ruhin yaƙinsu na da ƙarfi.

Ya kuma gode da goyon bayan al’umma wajen bayar da muhimman bayanai da suka kai ga nasarar aikin.

“Har zuwa lokacin fitar da wannan sanarwar, lamarin yana ƙarƙashin iko, yayin da ake ci gaba da sa ido don hana aukuwar wasu lamurra.

“An umarci rundunar da ta ci gaba da ƙara ƙoƙari wajen tabbatar da tsaron yankin don kare rayuka da dukiyoyi,” a cewar sanarwar.

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Gadar Da Sin Ta Gina Ta Inganta Yawon Bude Ido A Tsibirin Kasar Mozambique

Gadar Da Sin Ta Gina Ta Inganta Yawon Bude Ido A Tsibirin Kasar Mozambique

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.