• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ceto Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Boko Haram Suka Sace, Ruth Bitrus, A Borno

by Muhammad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Ceto Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Boko Haram Suka Sace, Ruth Bitrus, A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojojin Nijeriya sun ceto wata ‘yar makarantar Chibok mai suna, Ruth Bitrus, da aka yi garkuwa da ita tare da wasu da dama daga makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati ta Chibok da ke Jihar Borno a ranar 14 ga Afrilu, 2014.

Wani rahoton sirri da Zagazola Makama, masani a fannin yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a tafkin Chadi, ya samu daga majiyar sojin, wanda ya riski wakilinmu, ya nuna cewa Sojojin Birged 21 masu sulke ne suka ceto Ruth da danta a Bama, jihar Borno ranar Laraba, 29 ga watan Yuni, 2022, bayan ta tsere daga hannun mayakan Boko Haram a yankin karamar hukumar Bama ta jihar.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 3 Da Kwato Makamai A Wani Farmaki Da Suka Kai Musu
  • ‘Yan Boko Haram 204 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Jihar Borno

A yayin da take bayar da labarin irin halin da ta shiga, Ruth ta ce ta tsere daga dajin Sambisa shekaru takwas bayan da ‘yan ta’addar Boko Haram suka sace ta daga makarantarta da ke garin Chibok.

Ta ce bam ne ya kashe mijin ta ‘dan ta’adda a lokacin da yake kokarin tayar da shi a kan dakarun Operation Hadin Kai da ke yankin Arewa maso Gabas.

Ruth ta kara da cewa har yanzu sauran ‘yan matan makarantar na tare da wadanda suka yi garkuwa da su a dajin Sambisa.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

“Na dauki kwanaki uku ina tserewa daga yankin ‘yan tada kayar bayan. Na dauki abinci da zamu ci ni da yarona. Wasu daga cikin ‘yan Boko Haram sun ganni a lokacin da nake fitowa amma sai na gudu daji don gudun kada a kama ni,” inji ta.

Idan dai za a iya tunawa, makonni biyu da suka gabata ne Sojojin suka kubutar da wasu ‘yan matan makarantar Chibok guda biyu, Mary Dauda da Hauwa Joseph, bayan da suka tsere daga sansanin Gazuwa, hedikwatar kungiyar Jama’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād da aka fi sani da kungiyar Boko Haram. Gabchari da Mantari da Mallum Masari da ke da nisan kilomita tara zuwa karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Kubucewar nasu ya biyo bayan gagarumin farmakin da dakarun Operation Hadin Kai suka ci gaba da kaiwa, wanda ya janyo yunwa da kaura a yankunan ‘yan ta’addan.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Boko Haram ta yi garkuwa da dalibai mata 276, masu shekaru tsakanin 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno a watan Afrilun 2014.

Sama da 100 daga cikin ‘yan matan makarantar ne har yanzu ba a san inda suke ba tsawon shekaru takwas bayan da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan makarantaBarnoChibokMaiduguriSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kiki-kakar Mallakar Makami A Zamfara…

Next Post

A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

2 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

13 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

22 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

1 day ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 day ago
Next Post
Sojoji

A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.