Dakarun Sojojin Nijeriya sun samu nasarar daƙile wani harin ba-zata da mayaƙan ƙungiyar ISWAP suka kai a wani sansanin sojoji da ke garin Magumeri a Jihar Borno. Sai dai kuma, sojoji biyu sun rasa rayukansu a yayin wannan mummunar gwabzawa da ta faru a Arewa maso Gabas.
A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar ‘Operation Haɗin Kai’, Sani Uba ya fitar, ya bayyana cewa maharan sun nemi kutsawa cikin sansanin ne a lokacin da yanayin gari ya yi duhu sosai. Koda yake mayaƙan sun samu nasarar shiga wani ɗan bangare na sansanin a farkon harin, amma sojojin da ke bakin aiki suka yi wuf suka tunkare su da musayar wuta mai tsanani.
Sanarwar ta ƙara da cewa wannan namijin ƙoƙarin na sojojin ya tilasta wa ‘yan ta’addan arcewa daji ɗauke da raunukan harbin bindiga daban-daban, inda suka kasa cinma burinsu na mamaye wannan muhimmin sansani na sojojin.
A halin yanzu, rundunar sojin ta tsaurara matakan tsaro a yankin na Magumeri, wanda ke da tazarar kilomita 40 kacal daga birnin Maiduguri. An kuma tura ƙarin dakaru zuwa yankin don bayar da kariya tare da gudanar da aikin kakkaɓe dazuzzukan da ke kewaye don zaƙulo sauran ‘yan ta’addan da suka tsere.














