Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya gana da abokin takararsa, Hayatu-Deen, a gidansa da ke Lagos domin sasanta rikice-rikicen da suka biyo bayan zaben fidda gwani na shugaban ƙasa da ya janyo ce-ce-ku-ce a cikin jam’iyyar.
Ganawar ta zo ne bayan zaɓen fidda gwani da ya bai wa Atiku tikitin takarar shugaban ƙasa na ADC a 2027. Kafin sanar da sakamakon zaɓen, Hayatu-Deen ya janye daga takarar, inda ya yi zargin maguɗin zaɓe da kuma take haƙƙin masu kaɗa ƙuri’a a wasu sassan ƙasar.
Duk da ƙorafe-ƙorafe da ya gabatar, jam’iyyar ta ci gaba da bayyana sakamakon zaben, inda Atiku ya samu ƙuri’u 1,846,370, yayin da Rotimi Amaechi ya zo na biyu da ƙuri’u 504,117, sannan Hayatu-Deen ya samu ƙuri’u 177,120. Amaechi ma ya yi watsi da sakamakon, yana mai zargin an tafka kura-kurai da rashin adalci a tsarin zaɓen.
Tun bayan samun tikitin takara, Atiku ya fara tuntuɓar manyan jiga-jigan jam’iyyar domin haɗa kan mambobi kafin zaɓen 2027. A nasa ɓangaren, shugaban ADC, David Mark, ya dage cewa zaɓen ya kasance cikin adalci, duk da amincewarsa cewa ba a rasa wasu matsaloli ba. Ya ce dukkan ‘yan takarar sun cancanci jagorantar jam’iyyar, amma dole ne mutum ɗaya kacal ya zama ɗan takararta na shugaban ƙasa.















Discussion about this post